Yansanda a birnin Lagos na kudancin kasar sun kama wasu yan kasar Pakistan biyu wadanda suke da hannu dumu-dumi a cikin aikin kamawa don neman kudaden fansa daga hannun wani dan kasar ta Pakistan dan shekara 48 a duniya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran sun nakalto daga kafafen yada labaran kasar wadanda suka ji kakakin yansan na jihar Lagos Chief Superintendent Benjamin Hundeyin yana cewa, yan kasar Pakisatn da suka kama a wani dauki da suka wanda aka sace don neman kudaden fansa sun kama a ranar 5 ga watan maris akwia Roman Gull dan shekara 19 da kuma Aftab Ahmed dan shekarera 28 a duniya kuma yan asalin kasar Pakistan ne, wadanda suka hada kansu da wasu gungun barayi don yin haka.

Ya ce barayin sun nemi dalar Amurka $34,000 ko naira miliyon 50 daga wajensa a matsayin kudaden fansa. Amma kamfanin da yake yiwa aiki sun bada naira miliyon guda kacal a cikin kwanaki uku, inda yan sanda suka shiga suka kuma kubutar da shi. Kuma yansanda suna kokarin gano sauran mutane 5 da suke rage cikin gungun yan fashin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani

Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya sanar da sake haka sabbin rijiyoyin man fetur guda hudu yankin Kolmani na jihar Bauchi, kamar yadda Darakta a kamfanin, Yusuf Usman ya tabbatar.

Daraktan ya kuma sake jaddada aniyar kamfanin ta ganin ya fara aikin hako danyen man fetur a Arewacin Najeriya.

Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura

Ya bayyana hakan ne ranar Laraba a Kaduna a rana ta biyu ta taron tattaunawa tsakanin gwamnati da jama’a da Gidauniyar Tunawa da Ahmadu Bello ta shirya.

Daraktan ya ce, “Ya zuwa yanzu, NNPCL ya tono sabbin rijiyoyin danyen man fetur guda hudu a yankin Kolmani na jihar Bauchi, kuma yan kan aikin tantance fasahar da ta fi dacewa a yi aiki da ita a mataki na gaba a aikin.

“A wani yunkurinmu kuma na taimaka wa shirin Shugaban Kas ana komawa amfani da ababen hawa masu amfani da makamashin iskar gas a maimakon man fetur, yanzu haka ana can ana aikin gina tashoshin canza motoci zuwa masu amfani da gas na CNG da LNG,” in ji shi.

Ya ce da zarar an kammala aikinsu, ana sa ran tashoshin za su taimaka wajen bunkasa samuwar gas din kuma cikin sauki a Arewacin Najeriya.

Yusuf ya kuma zayyana wasu muhimman ayyuka da nasarorin da kamfanin ya samu a Arewacin Najeriya da ma sauran sassan kasar a karkashin mulkin Shugaban Kasa Bola Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar
  • Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa