Aminiya:
2025-07-31@14:05:15 GMT

Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90% a jihar

Published: 27th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya sanar da rage kashi 90% na tallafin rabon kayan abinci don ƙarfafa dogaro da kai a tsakanin mazauna jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da yake ƙaddamar da rabon kayan abinci ga magidanta 25,000 gabanin watan Ramadan a Maiduguri, Jere da sauran sassan jihar.

Helikwaftan farko ƙirar Najeriya zai fara aiki —NASENI Sarkin Musulmi ya ba da umarnin dubin watan Ramadan

A cewar Zulum, gwamnatin jihar za ta ba da fifiko ga hanyoyin samar da ci gaba na tsawan lokaci a kan matakan agaji na gajeren lokaci kamar rabon tallafin abinci.

Ya kuma bayyana irin gagarumin jarin da gwamnatinsa ta yi wajen tallafa wa manoma sama da miliyan ɗaya da muhimman kayayyakin amfanin gona kamar irin su iri, taki, famfunan ban-ruwa, maganin ƙwari da magungunan kashe ciyawa.

“Wannan dabarar ba kawai za ta inganta dogaro da kai ba ce har ma da rage kashe kuɗaɗen gwamnati,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, rabon kayan tallafin zai taƙaita ne ga ƙananan hukumomin jihar guda biyu kawai daga cikin 27  a shekarar 2025 saboda ƙalubalen da suke fuskanta.

“Ƙananan Hukumomin da za su sami tallafin abinci a shekara mai zuwa su ne: Ngala da Kala-Balge saboda yanayi na musamman.

“Waɗannan yankuna sun fuskanci mummunar ɓarna a gonakinsu daga giwaye kuma sun fuskanci ambaliyar ruwa. Don haka, a shekarar 2025, gwamnatin Jihar Borno za ta samar da kayayyakin tallafin abinci ga Ngala da Kala-Balge kaɗai,” inji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Umara Zulum Umara

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga

Bayo Onanuga, Mai Bai Wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, ya ce wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu ne kawai saboda ya fito daga Kudancin Najeriya.

Yayin wata hira da Trust Radio, Onanuga ya ce maganar cewa ana yi wa Arewacin Najeriya wariya ba gaskiya ba ce, face tsantsar siyasa kawai.

Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya

Ya ce ƙorafin da Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF), ta yi na cewa an yi watsi da Arewa wajen naɗe-naɗen muƙaman gwamnati da ayyukan ci gaba, wata dabara ce kawai don rage ƙimar shugabancin wanda ya fito daga Kudu.

Ya shawarci ’yan siyasar Arewa da su yi haƙuri, kamar yadda ɓangare Kudu ya yi lokacin mulkin marigayi Muhammadu Buhari, wanda ya shugabanci ƙasar har na tsawon shekaru takwas.

“Shugaba Tinubu ɗan Najeriya ne kamar kowa. Ya cancanci yin shekaru takwas a kan mulki kamar yadda Buhari ya yi. Ka da mu lalata ƙasa saboda son zuciya,” in ji Onanuga.

Dangane da zargin cewa an fi bai wa ’yan Kudu muƙamai, Onanuga ya ce masu sukar Tinubu su kawo hujjoji da ƙididdiga maimakon su ci gaba da yin zargin da ba shi da tushe.

Ya ƙara da cewa babu wani yanki da ba shi da matsalar hanyoyi ko ayyukan da ba a kammala gama ba, amma ya ce gwamnatin yanzu na ƙoƙarin gyara abubuwan da ta gada.

“Kafin ku zargi gwamnati, sai ku binciki gaskiyar lamarin. Wannan duk siyasa ce kawai don a raina Shugaban Ƙasa,” in ji shi.

Onanuga, ya kuma kare matakin da Tinubu ke ɗauka wajen inganta tsaro.

Ya ce an samu ci gaba sosai, inda ya kafa misalin cewar dukkanin shugabannin tsaro daga yankin Arewa suka fito.

Ya ce yanzu yana iya yin tafiya daga Kaduna zuwa Abuja cikin kwanciyar hankali, tafiyar da a da ta ke da hatsari sosai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
  • Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021