Aminiya:
2025-07-31@13:59:09 GMT

An yi wa mutane damfarar Naira biliyan 52 ta banki —NIBSS

Published: 27th, February 2025 GMT

Damfarar da aka yi wa mutane ta hanyar tura kuɗi ta banki ya ninku sau uku zuwa Naira biliyan 52 a Najeriya.

Alƙaluma ‘n Hukumar Kula da Tsarin Tura Kuɗi Tsakanin Bankuna (NIBSS) ya nuna a shekara huɗu da suka gabata aka samu wannan karin daga Naira biliyan 11 zuwa biliyan 52,

Alƙaluman sun nuna a shekara shekarar 2024 an yi asarar Naira biliyan 52, kusan ninki biyar na Naira biliyan 11,2 da aka yi asara a shekarar 2020.

Rahoton na NIBSS ya bayyana cewa masu damfarar sun yi yunƙurin sace Naira biliyan 86.4 a shekarar 2024.

 

The figure is coming on the heels of the latest GDP figures released by the National Bureau of Statistics showing a fourth quarter 2024 growth of 3.8 percent, the fastest in three years, driven by the services sector, including finance and insurance.

“Satar da ’yan damfara suka yi wa mutane ta hanyar hadahadar kuɗi ta zamani ta ƙaru saidai a cikin shekaru biyar da suka gabata,” in ji rahoton na NIBSS.

Ya ci gaba da cewa, “’yan damfarar na amfani da dabaru iri-iri, ciki har da amfani da bayanan tsofaffi ko ƙananan yara ko ’yan ƙasashen waje ko kuma a bayanan mutane ba da saninsu ba, wajen buɗe asusun banki.

“An gano yadda aka sace Naira miliyan 400 ta hanyar amfani da asusun da aka buɗe da bayanan mutane ba da saninsu ba ko kuma tsofaffi,” in ji rahoton.

Ya bayyana cewa an yi nasarar ƙwato wasu daga cikin kuɗaɗen sannan ana b’cingabda bincikar jami’an bankin da ake zargin hannunsu a badaƙalar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara tura kuɗi ta banki Naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

Har ila yau, Ribadu ya ce yanzu mutane suna iya zuwa gonakinsu a wuraren da a baya ba a iya shiga saboda barazanar ‘yan bindiga.

Sai dai duk da wannan ikirari, har yanzu wasu yankunan kamar Zamfara, Benuwe da Filato na fama da hare-haren ‘an bindiga da rikicin ƙabilanci.

A ƙarshen makon da ya gabata, ‘yan bindiga sun kashe mutane a Kauran Namoda a Jihar Zamfara.

Sannan ƙungiyar Boko Haram har yanzu na ci gaba da zama barazana a Arewa Maso Gabas.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata