An yi wa mutane damfarar Naira biliyan 52 ta banki —NIBSS
Published: 27th, February 2025 GMT
Damfarar da aka yi wa mutane ta hanyar tura kuɗi ta banki ya ninku sau uku zuwa Naira biliyan 52 a Najeriya.
Alƙaluma ‘n Hukumar Kula da Tsarin Tura Kuɗi Tsakanin Bankuna (NIBSS) ya nuna a shekara huɗu da suka gabata aka samu wannan karin daga Naira biliyan 11 zuwa biliyan 52,
Alƙaluman sun nuna a shekara shekarar 2024 an yi asarar Naira biliyan 52, kusan ninki biyar na Naira biliyan 11,2 da aka yi asara a shekarar 2020.
Rahoton na NIBSS ya bayyana cewa masu damfarar sun yi yunƙurin sace Naira biliyan 86.4 a shekarar 2024.
The figure is coming on the heels of the latest GDP figures released by the National Bureau of Statistics showing a fourth quarter 2024 growth of 3.8 percent, the fastest in three years, driven by the services sector, including finance and insurance.
“Satar da ’yan damfara suka yi wa mutane ta hanyar hadahadar kuɗi ta zamani ta ƙaru saidai a cikin shekaru biyar da suka gabata,” in ji rahoton na NIBSS.
Ya ci gaba da cewa, “’yan damfarar na amfani da dabaru iri-iri, ciki har da amfani da bayanan tsofaffi ko ƙananan yara ko ’yan ƙasashen waje ko kuma a bayanan mutane ba da saninsu ba, wajen buɗe asusun banki.
“An gano yadda aka sace Naira miliyan 400 ta hanyar amfani da asusun da aka buɗe da bayanan mutane ba da saninsu ba ko kuma tsofaffi,” in ji rahoton.
Ya bayyana cewa an yi nasarar ƙwato wasu daga cikin kuɗaɗen sannan ana b’cingabda bincikar jami’an bankin da ake zargin hannunsu a badaƙalar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Damfara tura kuɗi ta banki Naira biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
Sojojin Najeriya sun kashe aƙalla mayakan ƙungiyar ISWAP 8, ciki har da manyan kwamandojinta biyu a Jihar Borno.
Wata majiyar leƙen asiri daga rundunar haɗin kai ta OPHK ta bayyana cewa an kashe ’yan ta’addan ne a wata arangama da suka yi da sojojin a kan hanyar Maiduguri zuwa Baga a safiyar ranar Litinin.
DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabalaA cewar majiyoyin, an yi arangamar ce a kusa da Garin Giwa da ke gab da ƙauyen Kauwa, lokacin da ’yan ta’addan suka yi wa dakarun da ke sintiri kwanton ɓauna.
“A yayin wannan artabu, an kashe ’yan ta’adda takwas, ciki har da Munzirs biyu (kwamandojin filin daga na ƙungiyar) da kuma Qaid ɗaya (shugaban sashe).
“An kashe Modu Dogo, Munzir daga Dogon Chukun, wani Munzir da ba a bayyana ba, da Abu Aisha, shugaban sashe (Qaid) daga Tumbun Mota,” in ji wata majiya.
Majiyar ta ƙara da cewa wasu mayaƙa da dama sun samu raunuka, musamman waɗanda suka tsere da ƙafa bayan sun yi watsi da babura 14 da sojojin suka ƙwato.