An yi wa mutane damfarar Naira biliyan 52 ta banki —NIBSS
Published: 27th, February 2025 GMT
Damfarar da aka yi wa mutane ta hanyar tura kuɗi ta banki ya ninku sau uku zuwa Naira biliyan 52 a Najeriya.
Alƙaluma ‘n Hukumar Kula da Tsarin Tura Kuɗi Tsakanin Bankuna (NIBSS) ya nuna a shekara huɗu da suka gabata aka samu wannan karin daga Naira biliyan 11 zuwa biliyan 52,
Alƙaluman sun nuna a shekara shekarar 2024 an yi asarar Naira biliyan 52, kusan ninki biyar na Naira biliyan 11,2 da aka yi asara a shekarar 2020.
Rahoton na NIBSS ya bayyana cewa masu damfarar sun yi yunƙurin sace Naira biliyan 86.4 a shekarar 2024.
The figure is coming on the heels of the latest GDP figures released by the National Bureau of Statistics showing a fourth quarter 2024 growth of 3.8 percent, the fastest in three years, driven by the services sector, including finance and insurance.
“Satar da ’yan damfara suka yi wa mutane ta hanyar hadahadar kuɗi ta zamani ta ƙaru saidai a cikin shekaru biyar da suka gabata,” in ji rahoton na NIBSS.
Ya ci gaba da cewa, “’yan damfarar na amfani da dabaru iri-iri, ciki har da amfani da bayanan tsofaffi ko ƙananan yara ko ’yan ƙasashen waje ko kuma a bayanan mutane ba da saninsu ba, wajen buɗe asusun banki.
“An gano yadda aka sace Naira miliyan 400 ta hanyar amfani da asusun da aka buɗe da bayanan mutane ba da saninsu ba ko kuma tsofaffi,” in ji rahoton.
Ya bayyana cewa an yi nasarar ƙwato wasu daga cikin kuɗaɗen sannan ana b’cingabda bincikar jami’an bankin da ake zargin hannunsu a badaƙalar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Damfara tura kuɗi ta banki Naira biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
A Kaduna, an kama wasu mutane uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, ciki har da wani da ya ce ya koma jihar ne domin kafa sabuwar ƙungiya bayan an kama abokan aikinsa a Kwara.
Haka kuma, an kama wasu biyu da ke ɗauke da bindigogi.
‘Yansanda sun gano makamai da dama, ciki har da bindigogi ƙirar AK-47 da AK-49, da kuma wasu makamai da aka ƙera a gida.
Wannan aiki na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na yaƙar garkuwa da mutane da safarar makamai a faɗin ƙasar.
Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya ce ana ci gaba da bincike, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargi a kotu da zarar an kammala binciken.
Ya kuma yaba da goyon bayan da al’umma da jami’an tsaro suka bayar wajen nasarar kama su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp