HausaTv:
2025-08-12@12:49:57 GMT

Kungiyar RSF da kawayenta na shirin kafa gwamnatin ‘yan tawaye a Sudan

Published: 24th, February 2025 GMT

Kungiyar Rapid Support Forces na Sudan (RSF) sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya tare da kawayenta na kafa gwamnati ta bai daya, a cewar majiyoyin AFP, ba tare da yin la’akari da gargadin da aka yi cewa irin wannan matakin zai raba kasar da yaki ya daidaita ba.

Yarjejeniyar, wacce aka rattaba hannu a kanta a bayan fage a Nairobi babban birnin kasar Kenya, za ta kai ga samar da gwamnatin adawa a kasar Sudan, wadda za ta hada kungiyoyin  Rapid Support Forces, United Civil Forces, da kungiyoyin kwararru, da kuma SPLM-N.

Kamfanin dillancin labaran AFP ya ce, wannan yarjejeniya ta yi kira ga kafa gwamnati mai zaman kanta, da dimokuradiyya, daidaito, da adalci, ba tare da nuna bambanci ga kowane al’adu, kabila, addini, ko yanki ba.

Gwamnatin da aka gabatar na shirin magance gibin ayyuka a yankunan RSF a cewar Alaa El-Din Nuqd, wanda ya jaddada cewa “An katse al’ummar wadannan yankuna daga muhimman ayyuka kamar sabbin takardun kudi da sojoji suka fitar, sarrafa fasfo, da sabunta takardu,” kamar yadda kamfanin dillancin labaran AFP ya nakalto.

Mai magana da yawun rundunar RSF Najm al-Din Drisa ya ce za a iya kafa sabuwar gwamnati nan da wata guda.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dinkin Duniya Ta Sanar Da Mutuwan Mutane 60 Saboda Yunwa A El-Fasher Na Sudan

Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da cewa: Mutane 60 ne suka rasa rayukansu sakamakon yunwa a birnin El Fasher na Sudan

Ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya, OCHA, ya bayyana damuwarsa kan rahotannin da ke fitowa daga birnin El Fasher da ke arewacin Darfur, da ke cewa sama da mutane 60 sun mutu sakamakon yunwa da rashin abinci mai gina jiki cikin mako guda.

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya ya tabbatar da cewa ya fara tattara bayanan yunwa a sansanin Zamzam na ‘yan gudun hijira a Arewacin Darfur kimanin shekara guda da ta wuce, kuma ya jaddada cewa yana sa ran za a iya yada yunwa a wasu yankuna. A wani labarin kuma, Majalisar Dinkin Duniya ta tabbatar da cewa, abokan huldarta na cikin gida sun ba da rahoton mutane sama da 5,300 da ake zargi da kamuwa da cutar kwalara, inda mutane 84 suka mutu tun daga ranar 21 ga watan Yuni, yawancinsu a yankin Tawila, inda mutane 330,000 da suka rasa matsugunansu suke zaune a sansanin Zamzam da birnin El Fasher.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Iraki sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro August 12, 2025 Masar ta yi gargadin daukar tsauraran matakai domin kare muradunta August 12, 2025 Iran ta yi Allah wadai da kisan kiyashin da Isra’ila ta yi wa ‘yan jarida a Gaza August 12, 2025 Gaza: Yunwa ta kashe Falastinawa 5 a cikin kasa da Sa’o’i 24 da suka gabata August 12, 2025 Ministan tsaron Italiya ya caccaki gwamnatin Netanyahu kan batun Gaza August 12, 2025 Araghchi: Mataimakin Shugaban IAEA Zai Ziyarci Tehan َA Wannan Talata August 11, 2025 Iran: Lebanon Tana Da ‘Yancin Kare Kanta Da Makamanta August 11, 2025 Mali: An Kama Sojoji Fiye da 40 Bisa Zargin Yunkurin Juyin Mulki August 11, 2025 Iraki: Larijani Da Sudani Sun Gana A Bagdaza August 11, 2025 Mafi yawan Kasashen Duniya Sun Amince Da Samarda Kasar Falasdinu August 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Sanar Da Mutuwan Mutane 60 Saboda Yunwa A El-Fasher Na Sudan
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
  • Yajin Aikin NLC Da TUC Ya Gurgunta Ayyukan Gwamnati A Taraba.
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
  • Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba
  • An Zabi Alkalan Wasa Biyu Daga Kasar Iran Don Alkalanci A gasar Kwallon Kafa ta Mata
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi
  • Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Katin Duba Sakamakon Jarabawa Kyauta Ga Ɗalibai
  • Shugaban Kwango, Tshisekedi Ya Shigar Yan Tawaye A Gwamnatinsa