Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Al’umma Da Su Rika Taimakawa Hukumomin Tsaro Da Muhimman Bayanai
Published: 24th, February 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ‘yan Najeriya da su rika ba da muhimman bayanai ga hukumomin tsaron kasar nan.
Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake jawabi a wani taron jama’a na gwamnatin jihar Jigawa da aka gudanar a karamar hukumar Birnin Kudu.
A cewar sa, kiran ya zama wajibi domin karfafa tsaro a fadin Najeriya.
Alhaji Badaru Abubakar, ya yi nuni da cewa an samu ingantuwar harkokin tsaro a fadin kasar cikin ‘yan watannin nan.
Ya kuma bayyana cewa, gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi iya bakin kokarinta wajen yaki da rashin tsaro, kuma za ta ci gaba da jajircewa wajen cimma manufofin da ake so.
Ministan ya yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya za ta ci gaba da bayar da duk wani tallafi ga sojojin Najeriya da ke fagen fama don tabbatar da an maido da tsaro.
Badaru Abubakar wanda shi ne tsohon gwamnan jihar Jigawa, ya bayyana jin dadinsa da yadda ya mika ragamar shugabanci ga gwamnati mai inganci.
Ya yabawa gwamnatin Gwamna Umar Namadi bisa gagarumin ayyukan raya kasa da aka gudanar a jihar cikin shekara daya da rabi.
“Na yi farin cikin ganin manyan ayyukan raya kasa da wannan gwamnati ta aiwatar, a cikin shekara daya da rabi da ta wuce,” in ji Ministan.
Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, mataimakin gwamnan jihar, Injiniya Aminu Usman, da tsohon gwamnan jihar Barista Ali Sa’ad Birnin Kudu, da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim, da sarakuna da malaman addinai, da manyan jami’an gwamnati da dai sauransu.
Usman Muhammad Zaria.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Ministan Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
Tsarin yanayin masana’antu na Masar yana bunkasa kan fitar da kayayyaki zuwa Turai da Gabas ta Tsakiya. Tare da kasancewa mai karfi a cikin sinadarai, siminti, da kantin magani, Masar ta sanya kanta a matsayin jagorar masana’antun nahiyar da ke goyan bayan gyare-gyaren masana’antu.
An san kasar da samar da siminti, yadudduka, magunguna, da sinadarin man fetur da sauransu.
Sai kuma kasar Nijeriya mai rike da kambu na uku wacce ta kasance mai samun habaka a bangaren kasuwanci da masana’antu. Kamfanonin Dangote, musamman matatarsa da kuma rukunin kamfanonin BUA sun taimaka wa kasar wajen jan ragamar a bangaren masana’antu.
Manyan masana’antun kasar nan sun hada da na siminti, kayayyakin mabukata, abinci da abin sha, da tace mai, wanda manyan masana’antun kamar Dangote Group, BUA Group, Nestlé Nigeria, da Unileber Nigeria ke gudanarwa.
Morocco kuwa babbar cibiyar masana’antu ce a Arewacin Afirka, tana jawo hannun jari kai tsaye daga ketare a manyan masana’antu kamar kera motoci da hada-hadar jiragen sama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp