MD. Abdullahi ya ce ita gwamnati a tsare-tsarenta ba ta neman kamfanoni, kuma rashin neman kamfanoni ke hana samun nasara wajen tsara yanda za a tallafa wa manoma na samun saukin taki da yanda za su biya.

 

 

.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Amnesty International, ta ce Gwamnatin Tarayya ta yi sakaci game da ɓacewar ɗan gwagwarmaya Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.

A wata sanarwa da ta fitar, Amnesty, ta ce abin takaici ne ganin cewa shekara shida kenan da Dadiyata ya ɓace ba tare da wani sahihin bayani ba.

Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a Neja

Dadiyata ya ɓace ne a ranar 2 ga watan Agustan 2019, bayan wasu mutane ɗauke da makamai sun shiga gidansa da ke unguwar Barnawa a Jihar Kaduna, suka tafi da shi.

Tun daga wannan lokacin, iyalansa da abokansa ke jiran jin wani abu game da ɓacewarsa, amma har yanzu babu bayani.

Shugaban Amnesty a Najeriya, Isa Sanusi, ya ce Dadiyata mutum ne mai kishin ƙasa kuma yana da kishi wajen faɗin gaskiya a kafafen sada zumunta.

Ya ce akwai yiwuwar ɓacewar Dadiyata na da alaƙa da irin sukar da yake yi wa gwamnati da wasu ‘yan siyasa.

Ko da yake gwamnati ta musanta cewa tana da hannu, Amnesty ta ce dole gwamnati ta ɗauki alhakin binciken abin da ya faru da bayyana gaskiya domin rage wa iyalan Dadiyata raɗaɗi.

Ƙungiyar ta kuma buƙaci hukumomin tsaro su yi bincike mai zurfi, su kuma bayyana sakamakon da suka samu.

Ta ce abin takaici ne a ce shekara shida kenan ba tare da wani bayani dangane da ɓacewarsa ba.

Hakazalika, Amnesty ta buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da ya sa baki cikin lamarin domin a san halin da ake ciki.

Ta ce lokaci na ƙurewa, iyalan Dadiyata suna buƙatar amsa guda ɗaya kan inda ya shiga.

Wanda suka halarci taron manema labaran sun haɗa da matarsa Khadija Lame da ƙaninsa Usman Idris.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
  • Wani Dan Siyasa Ya Shirya Addu’o’i Na Musamman Domin Samun Zaman Lafiya A Zamfara
  • Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi
  • Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
  • Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty
  • Zulum zai mayar da ’yan gudun hijira 5,000 Bama
  • Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
  • Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
  • Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa
  • Yadda binciken zargin tallafa wa Boko Haram ke tafiyar hawainiya a Majalisa