Fararen Fatar Kasar Afirka Ta Kudu Sun Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Trump
Published: 16th, February 2025 GMT
A jiya Asabar ne da wasu kungiyoyi na fararen fata a kasar Afirka ta kudu sun yi gangami a bakin ofishin jakadancin Amurka dake birnin Pretoria suna masu nuna goyon bayansu ga kalaman da Donald Trump da ya riya cewa, gwamnatin kasar da bakaken fata masu rinjaye tana nunawa fararen fata wariya.
Daruruwan masu gangamin sun daga kwalaye da aka yi rubuta a jikinsu da su ka kunshi yin godiya ga Donald Trump da ya yi Magana akan abinda ce, damuwarsu ce.
Wanda ya shirya gangamin Willem Petzer, ya ce, yana son fadawa kasashen turai cewa, suna da kawaye a cikin kasar Afirka ta kudu.
Da dama daga cikin mahalarta gangamin sun fito ne daga al’ummar Afirkana da Trump ya ce, gwamnatin kasar ta yi dokar kwace musu filaye.
Shi kuwa Heinrich Steinhausen ya bayyana cewa; A cikin shekaru 30 na bayan nan an sami rabuwar kawuna a cikin kasar saboda abinda ya kira siyasar gwamnati.
Tuni dai gwamantin kasar Afirka ta kudu ta yi watsi da wadannan zarge-zargen na Donald Trump.
Masu bin diddigin abinda yake faruwa suna ganin cewa Amurkan tana yin matsin lamba ne akan kasar Afirka ta kudu saboda ta shigar da kasar “Isra’ila” a gaban kotun duniya ta manyan laifuka da ta yanke hukunci akan Isra’ila da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Afirka ta kudu
এছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
Tsarin yanayin masana’antu na Masar yana bunkasa kan fitar da kayayyaki zuwa Turai da Gabas ta Tsakiya. Tare da kasancewa mai karfi a cikin sinadarai, siminti, da kantin magani, Masar ta sanya kanta a matsayin jagorar masana’antun nahiyar da ke goyan bayan gyare-gyaren masana’antu.
An san kasar da samar da siminti, yadudduka, magunguna, da sinadarin man fetur da sauransu.
Sai kuma kasar Nijeriya mai rike da kambu na uku wacce ta kasance mai samun habaka a bangaren kasuwanci da masana’antu. Kamfanonin Dangote, musamman matatarsa da kuma rukunin kamfanonin BUA sun taimaka wa kasar wajen jan ragamar a bangaren masana’antu.
Manyan masana’antun kasar nan sun hada da na siminti, kayayyakin mabukata, abinci da abin sha, da tace mai, wanda manyan masana’antun kamar Dangote Group, BUA Group, Nestlé Nigeria, da Unileber Nigeria ke gudanarwa.
Morocco kuwa babbar cibiyar masana’antu ce a Arewacin Afirka, tana jawo hannun jari kai tsaye daga ketare a manyan masana’antu kamar kera motoci da hada-hadar jiragen sama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp