Fararen Fatar Kasar Afirka Ta Kudu Sun Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Trump
Published: 16th, February 2025 GMT
A jiya Asabar ne da wasu kungiyoyi na fararen fata a kasar Afirka ta kudu sun yi gangami a bakin ofishin jakadancin Amurka dake birnin Pretoria suna masu nuna goyon bayansu ga kalaman da Donald Trump da ya riya cewa, gwamnatin kasar da bakaken fata masu rinjaye tana nunawa fararen fata wariya.
Daruruwan masu gangamin sun daga kwalaye da aka yi rubuta a jikinsu da su ka kunshi yin godiya ga Donald Trump da ya yi Magana akan abinda ce, damuwarsu ce.
Wanda ya shirya gangamin Willem Petzer, ya ce, yana son fadawa kasashen turai cewa, suna da kawaye a cikin kasar Afirka ta kudu.
Da dama daga cikin mahalarta gangamin sun fito ne daga al’ummar Afirkana da Trump ya ce, gwamnatin kasar ta yi dokar kwace musu filaye.
Shi kuwa Heinrich Steinhausen ya bayyana cewa; A cikin shekaru 30 na bayan nan an sami rabuwar kawuna a cikin kasar saboda abinda ya kira siyasar gwamnati.
Tuni dai gwamantin kasar Afirka ta kudu ta yi watsi da wadannan zarge-zargen na Donald Trump.
Masu bin diddigin abinda yake faruwa suna ganin cewa Amurkan tana yin matsin lamba ne akan kasar Afirka ta kudu saboda ta shigar da kasar “Isra’ila” a gaban kotun duniya ta manyan laifuka da ta yanke hukunci akan Isra’ila da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Afirka ta kudu
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
Gwamnatin kasar Iran ta bayyana wasu abubuwan da bata amince da su ba, a jawabin bayan taro na musamman na kungiyar kasashen musulmi ta (OIC) wanda aka gudanar a birnin Doha na kasar Qatar a ranar litinin 15 gawatan Satumba da mukeciki. Sannan ta kara tabbatar da goyon bayanta ga gwagwarmayan da Falasdinawa suke yi da HKI don kwatar kasarsu da ta mamaye.
A cikin wani bayanin da ma’aikatar harokokin wajen kasar Iran ta fitar a yau Laraba, Jumhuriyar Musulunci ta Iran, tana kara jaddada goyon bayanta ga al-ummar Falasdina, kuma tana kara jaddada tir da allawai da kissan kiyashin da HKI take yi a Gaza da kuma sauran yankunan falasdinawa da ta mamaye. Kuma tana godewa mutanen kasar Iran dangane da goyon bayan da suke bawa Falasdinawa a gwagwarmayansu da HKI.
Dangane da shawarorin da aka gabatar a taron OIC, Iran tana godiya kasashen musulmi da wadanda ba musulmi kan shawarorin da suka gabatar, don warware rikicin Falasdinawa, daga ciki har da “New York Declaration” ta samar da kasashe 2. Da wasu da dama. Amma JMI tana ganin kafa kasashe biyu bazai warware rikicin ba. Tana ganin gudanar da zaben raba gardama, a kasar wanda zai hada da dukkan falasnawa a ko ina suke a ciki da wajen kasar, don zabawa kansu tsari dairin gwamnati da suke su ta demucradiyya. Irab tana ganin samar da kasar Falasdinu a dukkan fadinkasar wacce take da dukkan birnin Qudus a matsayin babban birnin kasar ita ce mafita. Yahudawan da suke son zama su zauna wadanda suke son tafiya su koma kasarsu ta asalali.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Chadi: Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci