Aminiya:
2025-09-17@23:28:52 GMT

Yadda za a yaƙi talauci a Arewa maso Gabas  — Shettima

Published: 16th, February 2025 GMT

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya buƙaci Hukumar Bunƙasa Arewa maso Gabas (NEDC) da ma’aikatar raya yankuna ta tarayya da su magance talauci a yankin ta hanyar zuba jari a fannin ilimi.

Shettima ya yi wannan kiran ne a yayin wata ganawa da ya yi da mahukuntan hukumar ta NEDC a fadar shugaban kasa da ke Abuja, inda suka yi masa bayani kan wani shiri na harkokin ilimin babbar sakandare — ASSEP.

Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 a Borno Dalilin da ’yan siyasa ke sauya sheƙa zuwa APC — Tambuwal

Ya kuma yaba wa hukumar NEDC kan yadda ta ke ba da gudummawar a fannin ilimi, inda ya ce za a riƙa tunawa da irin wannan ƙoƙari a nan gaba.

Shettima ya kuma yi nuni da cewa, akwai matsanancin talauci a yankin Arewa maso Gabas, inda ya kwatanta shi da wasu yankunan da ke fama da talauci a duniya, yana mai alakanta bullar ƙungiyoyin tsageru a yankin da irin waɗannan yanayi na zamantakewa.

Duk da kalubalen, ya yaba wa hukumar ta NEDC da abokan huldar ta, ciki har da Dokta Mariam Masha, saboda aikin da suke yi na inganta shirin ASSEP, yana mai cewa akwai yiwuwar canza yanayin yankin.

Mataimakin shugaban ƙasar ya buƙaci hukumar NEDC, ma’aikatar raya yankuna, da sauran masu ruwa da tsaki da su haɗa kai don samun ingantaccen aiki da samun nasara wajen aiwatar da shirin na ASSEP.

A nasa ɓangaren, Ƙaramin Ministan ci gaban yankin, Uba Ahmadu, ya lura cewa shirin na ASSEP na da zummar inganta ilimin sakandare a yankin, tare da ajandar Shugaba Bola Tinubu na inganta matakan ilimi na ƙasa.

Manajan Daraktan Hukumar NEDC, Alhaji Mohammed Alkali, ya yi cikakken bayanin dangane irin ƙoƙarin da hukumar ke yi wajen bunƙasa rayuwar bil’adama, ciki har da horar da malamai da kafa cibiyoyin ilimin yanar gizo (ICT) a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato

Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, ya ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani guda 20, tare da riguna ruwa (life jackets) 2,000, domin rage haɗurran da ke aukuwa sakamakon ambaliya da nutsewar jirage a sassan jihar.

An ƙaddamar da jiragen ne a ƙaramar hukumar Wamakko a ranar Laraba, inda gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin shirin gaggawa na tallafa wa al’ummar da ke fama da illar ambaliya da haɗurra a ruwa.

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB

“Mun dauki wannan mataki bayan rahotannin da muke samu na yawaitar hatsarurruka da rasa rayuka da dukiya sakamakon jiragen katako da mutane ke amfani da su,” in ji Gwamna Ahmad Aliyu.

Gwamnan ya miƙa godiya ga shugabar hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), Hajiya Zubaida Umar, bisa hadin kai da goyon bayan da hukumar ke bayarwa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiya, tare da inganta ayyukan ceto da agaji a jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, an horar da direbobin jiragen ruwan da za su riƙa kula da su, kafin a raba su zuwa ƙananan hukumomi goma (10) da suka fi fuskantar barazanar ambaliya da suka haɗa da: Goronyo, Shagari, Sabon-Birni, Wurno, Rabah, Wamakko, Silame, Kebbe, Tambuwal da Isa.

Gwamnan ya kuma yi gargaɗin cewa za a hukunta duk wani da ya ɗauki lodi fiye da ƙima a cikin jiragen, yana mai cewa “wannan jirage da rigar ruwa na jama’a ne, kuma wajibi ne shugabannin ƙananan hukumomi su tabbatar da kula da su yadda ya kamata.”

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankunan da za a rabawa jiragen sun bayyana ra’ayinsu dangane da lamarin, inda wani Tanimu Goronyo, daga karamar hukumar Goronyo, ya ce: “Gwamnatin Sakkwato ta kauce hanya.

“Abin da muke bukata a yanzu shi ne hanyoyin mota da magudanan ruwa. Ambaliya tana mamaye yankunan mu ne saboda babu hanya. Idan gwamnati ta kashe wannan kuɗi wajen gina hanya, sai an fi cin moriya.”

Shi ma wani Muhammad Kabiru, daga Silame, ya bayyana farin cikinsa da sayen jiragen, sai dai ya roƙi gwamnati da ta mai da hankali wajen gina hanyoyin mota saboda abin da suka fi buƙata ke nan.

“Mu a Silame jirgi yana da amfani, amma hanyar mota ita ce babbar buƙatar mu. Idan aka samar da ita, ambaliya ba za ta hana mu zirga-zirga ba.”

Yayin da gwamnatin Sakkwato ke ɗaukar matakan gaggawa don rage hatsarurruka da ambaliya ke haifarwa, al’umma na ci gaba da neman tsarin da zai magance tushen matsalar – musamman samar da ingantattun hanyoyi da magudanan ruwa a karkara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago