Aminiya:
2025-08-01@09:19:41 GMT

Yadda za a yaƙi talauci a Arewa maso Gabas  — Shettima

Published: 16th, February 2025 GMT

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya buƙaci Hukumar Bunƙasa Arewa maso Gabas (NEDC) da ma’aikatar raya yankuna ta tarayya da su magance talauci a yankin ta hanyar zuba jari a fannin ilimi.

Shettima ya yi wannan kiran ne a yayin wata ganawa da ya yi da mahukuntan hukumar ta NEDC a fadar shugaban kasa da ke Abuja, inda suka yi masa bayani kan wani shiri na harkokin ilimin babbar sakandare — ASSEP.

Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 a Borno Dalilin da ’yan siyasa ke sauya sheƙa zuwa APC — Tambuwal

Ya kuma yaba wa hukumar NEDC kan yadda ta ke ba da gudummawar a fannin ilimi, inda ya ce za a riƙa tunawa da irin wannan ƙoƙari a nan gaba.

Shettima ya kuma yi nuni da cewa, akwai matsanancin talauci a yankin Arewa maso Gabas, inda ya kwatanta shi da wasu yankunan da ke fama da talauci a duniya, yana mai alakanta bullar ƙungiyoyin tsageru a yankin da irin waɗannan yanayi na zamantakewa.

Duk da kalubalen, ya yaba wa hukumar ta NEDC da abokan huldar ta, ciki har da Dokta Mariam Masha, saboda aikin da suke yi na inganta shirin ASSEP, yana mai cewa akwai yiwuwar canza yanayin yankin.

Mataimakin shugaban ƙasar ya buƙaci hukumar NEDC, ma’aikatar raya yankuna, da sauran masu ruwa da tsaki da su haɗa kai don samun ingantaccen aiki da samun nasara wajen aiwatar da shirin na ASSEP.

A nasa ɓangaren, Ƙaramin Ministan ci gaban yankin, Uba Ahmadu, ya lura cewa shirin na ASSEP na da zummar inganta ilimin sakandare a yankin, tare da ajandar Shugaba Bola Tinubu na inganta matakan ilimi na ƙasa.

Manajan Daraktan Hukumar NEDC, Alhaji Mohammed Alkali, ya yi cikakken bayanin dangane irin ƙoƙarin da hukumar ke yi wajen bunƙasa rayuwar bil’adama, ciki har da horar da malamai da kafa cibiyoyin ilimin yanar gizo (ICT) a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka

Sakatariyar kungiyar kasashen yankin Caribeans  ( Caricom) ta bayyana cewa; kasashen yankin suna son ganin bunkasa alakar kasuwanci da abokansu na nahiyar Afirka.

 Sakatariyar kuniyar ta kasashen Caribbian ta bayyana hakan ne a lokacin jawabin bude taron karawa juna sani a taron kasuwanci da zuba hannun jari a tsakanin yankin da nahiyar Afirka da aka yi a Grenada. Ta kuma kara da cewa:

 Wajibi ne mu bude sabuwar kafar kasuwanci a tsakanin yankunan biyu, kuma ya kamata ace giman kasuwanci a tsakanin bangarorin biyu ya karu da kaso 3% na jumillar kasuwancinmu.”

Kamfanin dillancin labarun “Reuters’ya bayyana cewa wannan matakin na kasashen Caribbean yana nuni da sauyi a huldarsa ta kasunwaci da Amurka da Canada da kuma kasashen turai da su ne abokansu na cinikayya.

  A cikin watan Aprilu ne dai kasar Amurka ta kakabawa dukkanin abokan kasuwancinta kudin fito da sun kai kaso 10%. Bugu da kari Amurkan tana da gagarumin tasiri a cikin harkokin kasuwanci da zuba hannun jari a cikin kasashen yankin na Caribbean.

 Amurka ce babbar abokiyar kasuwancin kasashen yankin Caribbean da take sayen kaso 1/4 na hajar da yankin ke fitarwa da kudin da sun kai dala biliyan 38.8, yayuin da yankin yake sayo kayayyakin da sun kai Dala biliyan 43.4 daga Amurka.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni
  • Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai