Gwamnatin Tarayya Za Ta Bada Tallafin Naira 75, 000 Ga Marasa Kafi A Jigawa
Published: 8th, February 2025 GMT
Shirin Inganta rayuwar al’umma na jihar Jigawa ya raba katinan cire kudi na ATM a kananan hukumomi 10 daga cikin 27 domin al’umma su sami tallafin naira dubu saba’in da biyar biyar na gwamnatin Tarayya.
Shugaban shirin na jihar, Malam Mustapha Umar Babura ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.
Yayi bayanin cewar, ana rabon katinan karbar kudin ne ga wadanda za su sami tallafin inganta rayuwa na naira dubu sabain da biyar.
A cewarsa, duk da korafe korafen da ake samu wajen rabon katinan, aikin na cigaba da gudana yadda ya kamata.
Mustapha Umar Babura ya ce ana ta kokarin warware duk matsalolin da ma’aikatan suke cin karo da su wajen rabon katinan ga al’umma.
Yana mai cewar, a zancen ma da ake yi yanzu, ana nan ana tsare-tsare na sake dawo da shirin ciyar da dalibai a makarantu.
Babura, ya ce duk mai korafi zai iya gabatar da shi ga jami’an shirin da ake da su a kananan hukumomin jihar 27 domin inganta ayyukan shirin.
Shugaban shirin inganta rayuwar al’umma na jihar Jigawa ya kara da cewar an bullo da shirin ne domin inganta rayuwar masu karamin karfi a jihar.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da naɗa Muhammad Fa’iz a matsayin Kwamanda Janar na farko na Hukumar Hisbah ta Jihar.
Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ne ya tabbatar da naɗin ga manema labarai a Dutse.
Ya bayyana cewa hakan na daga cikin ƙoƙarin Gwamna Namadi na ƙarfafa ayyukan sabuwar hukumar Hisbah da inganta aikinta.
A cewar sa, naɗin ya haɗa da Dr. Husaini Yusuf Baban a matsayin Babban Mataimakin Kwamanda Janar, da Lawan Danbala a matsayin Mataimakin Kwamanda Janar da hedikwatar hukumar, da kuma Yunusa Idris Barau a matsayin Mataimakin Kwamanda Janar naYankin Dutse.
Sauran su ne Abdulkadir Zakar, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Hadejia, da Suraja Adamu, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Gumel, da Bello Musa Gada, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Kazaure, sai Barrister Mustapha Habu a matsayin Sakatari kuma Lauya mai ba da shawara.
Malam Bala Ibrahim ya jaddada cewa an zaɓi waɗannan mutane ne bisa cancanta, ƙwarewa da kuma nagartar halayensu, yana mai kira gare su da su yi kokarin sauke nauyin da aka dora musu.
Sakataren Gwamnatin Jihar ya ce an riga an mika musu takardun naɗi kuma sun shirya tsaf don fara aiki nan take.
A nasa bangaren, Muhammad Fa’iz ya gode wa Gwamna bisa amincewar da ya nuna musu, tare da alƙawarin gudanar da aiki da ƙwazo da himma.
Usman Muhammad Zaria