Gobara ta yi ajalin almajirai 17 a Zamfara
Published: 5th, February 2025 GMT
Wata gobara da ta tashi a wata makarantar tsangaya da ke Ƙaramar Hukumar Kaura-Namoda a Jihar Zamfara, ta yi ajalin almajirai 17.
Dukkanin almajiran sun ƙone ƙurmus, ta yadda ba a gane kowa a cikinsu ba.
Saura ƙiris Bello Turji ya zo hannu – Ministan Tsaro Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trnShaidu sun bayyana cewa gobarar ta farq ne cikin daren ranar Talata, kuma ta ɗauki kimanin sa’o’i uku tana ci.
Rahotanni sun bayyana cewar wasu almajirai 16 sun samu munanan raunuka a gobarar.
Wani mazaunin yankin, Abdulrasaq Bello Kaura, ya bayyana cewa gobarar ta fara ne sakamakon kamawar wasu itatuwa da aka ajiye.
Wani ganau ya shaida cewar, “Abin ya faru ne a makarantar Malam Ghali, a cikin ɗakin karatu.
“Akwai kusan almajirai kusan 100 a cikin gidan. Bayan da aka fitar da su, sai aka ɗauka babu kowa a ciki.
“Amma bayan gobarar ta lafa, sai aka dawo aka ga sassan jikin wasu kamar ƙafafu, hannaye, da kuma gawarwakin waɗanda suka rasu bayan sun ƙone ƙurmus.”
An yi jana’izar waɗanda suka rasu a ranar Laraba.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Kaura-Namoda, Kwamared Mannir Muazu Haidara, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce yana kan hanyarsa ta zuwa wajen da lamarin ya faru domin samun ƙarin bayani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Almajirai Gobara Makarantar Tsangaya Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar
Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Uganda ta sanar da cewa, an kawo karshen Ebola da ta bulla a kasar bayan da aka dauki kwanaki 42 ba tare da an sami mutum daya wanda ya sake kamuwa da ita ba.
A wani bayani da ya fito daga hukumar kiwon lafiya ta duniya ( WHO), ta bayyana cewa, a lokacin bullar cutar an gabatar da mutane 14 masu dauke da ita, an tabbatar da 12 daga cikinsu, sai wasu biyu da ba a same ta a tare da su ba.”
Haka nan kuma hukumar lafiyar ta ce, an sami mutuwar mutane 4 daga cikin wadanda su ka kamu da cutar ta Ebola, wasu mutane 10 kuma sun warke.”
Watanni 9 da su ka gabata ne dai aka tabbatar da bullar cutar a birnin Kamfala bayan da wani mutum da yake dauke da ita ya rasu.
Dajukan da kasar ta Uganda take da su, suna a matsayin matattarar cutar ta Ebola ce, wacce a karon farko ta bulla a cikin kasar a 2000.
A yankin yammacin Afirka cutar Ebola ta kashe fiye da mutane 11,000 a tsakanin 2013 zuwa 2016.