Gobara ta yi ajalin almajirai 17 a Zamfara
Published: 5th, February 2025 GMT
Wata gobara da ta tashi a wata makarantar tsangaya da ke Ƙaramar Hukumar Kaura-Namoda a Jihar Zamfara, ta yi ajalin almajirai 17.
Dukkanin almajiran sun ƙone ƙurmus, ta yadda ba a gane kowa a cikinsu ba.
Saura ƙiris Bello Turji ya zo hannu – Ministan Tsaro Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trnShaidu sun bayyana cewa gobarar ta farq ne cikin daren ranar Talata, kuma ta ɗauki kimanin sa’o’i uku tana ci.
Rahotanni sun bayyana cewar wasu almajirai 16 sun samu munanan raunuka a gobarar.
Wani mazaunin yankin, Abdulrasaq Bello Kaura, ya bayyana cewa gobarar ta fara ne sakamakon kamawar wasu itatuwa da aka ajiye.
Wani ganau ya shaida cewar, “Abin ya faru ne a makarantar Malam Ghali, a cikin ɗakin karatu.
“Akwai kusan almajirai kusan 100 a cikin gidan. Bayan da aka fitar da su, sai aka ɗauka babu kowa a ciki.
“Amma bayan gobarar ta lafa, sai aka dawo aka ga sassan jikin wasu kamar ƙafafu, hannaye, da kuma gawarwakin waɗanda suka rasu bayan sun ƙone ƙurmus.”
An yi jana’izar waɗanda suka rasu a ranar Laraba.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Kaura-Namoda, Kwamared Mannir Muazu Haidara, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce yana kan hanyarsa ta zuwa wajen da lamarin ya faru domin samun ƙarin bayani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Almajirai Gobara Makarantar Tsangaya Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
Uwargidan Shugaban Nijeriya, Sanata Remi Tinubu ta bayar da tallafin naira biliyan daya ga wadanda harin nan ya rutsa da su a yankin Yelwata na Ƙaramar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.
Sanata Tinubu wadda ta miƙa cakin kuɗin ga Gwamna Hyacinth Alia ta sanar da bayar da tallafin ne a jawabinta na jaje wanda ta kai Fadar Gwamnatin Benuwe da ke Makurdi.
Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a ChinaUwargidan shugaban ƙasar ta buƙaci a yi amfani da wannan tallafin a matsayin gudunmawar farfaɗo da yankin da waɗanda suka tsallake rijiya da baya a yayin harin musamman yaran da yanzu ke buƙatar komawa makarantu.
Ana iya tuna cewa, tun a daren ranar 13 ga watan Yuni zuwa wayewar gari 14 ga watan ne aka kashe fiye da mutum 100 a ƙauyen Yelwata, lamarin da ya janyo Allah wadai daga sassa daban-daban a faɗin ƙasar.
Jihar Benuwe dai na daga cikin jihohin da ke fuskantar matsalar tsaro a Nijeriya, musamman rikicin manoma da makiyaya da kuma na ƙabilanci, wanda ke sanadiyyar salwantar rayuka da dama.