Ma’aunin Cinikayyar Ba Da Hidimomi Ta Sin Ya Zarce Dala Triliyan 1
Published: 4th, February 2025 GMT
Alkaluman da ma’aikatar cinikayya ta Sin ta fitar baya-bayan nan na cewa, a shekarar bara, darajar shige da ficen cinikayyar ba da hidimomi ta Sin ta kai kudin Sin RMB yuan triliyan 7.5, kwatankwacin dalar Amurka triliyan 1.034, wanda ya karu da kashi 14.4 cikin dari bisa makamancin lokaci na shekarar 2023, ma’aunin ya kai wani sabon matsayi a tarihi.
Shugaban hukumar kula da cinikayyar ba da hidimomi ta cibiyar nazarin hadin gwiwar ciniki da tattalin arziki na kasa da kasa ta ma’aikatar kasuwanci ta kasar, Li Jun, ya bayyana cewa, al’adun Sin masu kayatarwa na ci gaba da jawo hankalin masu yawon bude ido su zo kasar Sin don yawon shakatawa, da alamar zai inganta habaka ma’aunin cinikayyar ba da hidimomi ta Sin, tare da inganta da maido da aikin ba da hidimomin yawon shakatawa na kasa da kasa.
Bugu da kari, abubuwa da dandamalin da suka shafi al’adun dijital na kasar Sin sun taka rawar gani sosai a ketare. Misali, tun lokacin farko da aka fitar da shi a shekarar 2024, wani wasan kamfuta mai suna “Black Myth: Wukong” cikin sauri ya zama jagoran tallace-tallace a kan dandamalin wasannin kamfuta masu yawa kamar Steam da WeGame, kuma ya sami lambobin yabo da yawa.
Bisa rahoton binciken ci gaban adabi na intanet na kasar Sin a shekarar 2023, yawan labaran adabi na yanar gizo da ‘yan kasar Sin suka rubuta da kansu a ketare a shekarar 2023 ya kai kusan dubu 620, tare da masu karantawa da suka kai fiye da miliyan 230 a ketare.(Safiyah Ma)
এছাড়াও পড়ুন:
Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun kashe masu zaman makoki bakwai tare da jikkata wasu a ƙauyen Kopl da ke Ƙaramar Hukumar Chibok ta Jihar Borno.
Shugaban Karamar Hukumar, Honorabul Modu Mustapha, ya ce mayaƙan sun buɗe wa mutanen wuta ne a yammacin ranar Litinin, a yayin da suke shirin gudanar da addu’o’i ga ’yan uwansu da suka rasu.
Ya ce, “Sun taru ne domin yin addu’a lokacin da ’yan ta’addan suka sauka a kansu. Mun kwashe mutane da yawa da suka samu raunukan harsashi zuwa Babban Asibitin Mubi da ke maƙwabtaka da Jihar Adamawa.
“Adadin waɗanda suka mutu na iya ƙaruwa, saboda wasu sun tsere cikin daji da raunukan harsashi. Ana ci gaba da aikin nemowa da ceto waɗanda ke cikin daji,” in ji shi.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasuSanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ci gaba da yin Allah wadai da hare-haren, inda ya bayyana halin da ake ciki a matsayin abin da ya wuce tunanin dan Adam.
“Ko jiya ma, na samu kiran gaggawa cewa an kashe sama da ’yan banga 10 a wani yankin da ke tsakanin Karamar Hukumar Hawul ta Jihar Borno da garin Garkida a Jihar Adamawa.
“Al’ummata na fama da munanan asara ba tare da wani faɗa ba. A cikin wata guda da ya gabata kaɗai, an kashe sama da mutum dari a hare-hare da dama yankunan Sabon Gari da Izge da Kirawa da Pulka da Damboada Chibok da Askira Uba da wasu da yawa da ba zan iya lissafawa ba,” in ji Sanata Ndume.