Gwamnatin Isra’ila Tana Tsoron Kama Fira Ministanta Don Haka Ta Canja Tsarin Tafiyarsa Zuwa Amurka
Published: 3rd, February 2025 GMT
Gwamnatin mamayar Isra’ila ta tantance hanya ta musamman da jirgin da ya dauki fira ministan mamayar Isra’ila zuwa Amurka saboda tsoron kama shi!
A wani mataki da ke nuni da yadda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kara nuna damuwa, jaridar Ma’ariv ta haramtacciyar kasar ta watsa rahoton cewa: Jirgin da ke dauke da fira ministan haramtacciyar kasar, Benjamin Netanyahu zuwa birnin Washington na Amurka, ya dauki wata hanya ta musamman, domin ya gwammace ya kaucewa wucewa ta sararin samaniyar kasashe wadanda suka tabbatar da cewa ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen aiwatar da sammacin kama Netanyahu idan ya shiga sararin samaniyarsu.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya, bayan da kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta bayyana aniyar ta fitar da sammacin neman kame jami’an gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila kan hare-haren wuce gona da iri da ta kai kan Gaza, lamarin da ya dada nuna damuwar gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila kan yiwuwar daukar matakin shari’a kan shugabanninta yayin da suke balaguro zuwa kasashen waje.
Tun a jiya Lahadi ce Benjamin Netanyahu ya kama hanyar tafiya Amurka don ganawa da Donald Trump, a ziyarar aiki da ake sa ran za ta kai har zuwa ranar Alhamis.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: haramtacciyar kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bayyana cewa: Babu wata tattaunawa da zata yi da Amurka a halin da take ciki na kare kanta
A yayin da haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan yankunan kasar Iran, a hukumance Iran ta bayyana rashin yiwuwar ci gaba da zaman tattaunawa da Amurka kan batun shirinta na makamshin nukuliya, tare da dora wa Amurka alhakin abin da ke faruwa kai tsaye.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa: Akwai hadin kai tsakanin haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka wajen kai hare-hare kan kasar Iran domin rusa zaman tattaunawar nukiliya da haka ke bayyana kawar da duk wata magana ta hakikanin aniyar Amurka na samar da hanyar warware takaddamar Shirin Iran ta hanyar lumana.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa ci gaba da tattaunawa da Amurka a yayin da ake ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri yana gwada tsarin tattaunawar ba shi da ma’ana. Ya yi kakkausar suka ga matakin da hukumar ta IAEA ta dauka, inda ya yi la’akari da hakan a matsayin wani dalili na halasta cin zarafi a kan cibiyoyin nukiliyar Iran.