Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-16@01:04:28 GMT

Uwargidan Gwamnan Jigawa Ta

Published: 3rd, February 2025 GMT

Uwargidan Gwamnan Jigawa Ta

Uwargidan Gwamnan Jihar Jigawa, Hajiya Hadiza Umar Namadi ta kaddamar da wani katafaren  wurin shan shayi da taliya na zamani  a karamar hukumar Maigatari ta jihar.

Hajiya Hadiza Namadi ta ce, wurin sayar da shayin da taliyar da aka zamanantar da shi wani yunkuri ne na karamar hukumar ta Maigatari.

 

Ta kara da cewa, an tsara wannan wurin na zamani ne domin samar da yanayi mai kyau da inganci ga mutane, inda za su ci abinci cikin gamsuwa, tare da bunkasa kasuwanci a yankin.

Hajiya Hadiza ta kuma kaddamar wani tallafi ga mata 300 a karamar hukumar Maigatari.

 

An bayar da naira dubu talatin kowannensu, domin bunkasa kananan sana’o’i.

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, a yayin bikin, uwargidan gwamnan, Hajiya Hadiza Umar Namadi ta gabatar da takardun kama aiki na wucin gadi ga malaman makaranta su 173.

A zantawar wakilinmu da wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, sun yabawa shugaban karamar hukumar Maigatari bisa wannan karimcin.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Karamar hukumar Maigatari karamar hukumar Hajiya Hadiza

এছাড়াও পড়ুন:

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

Wakilin dindindin na kasar Sin a hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya ko IAEA Li Song, ya ce kasarsa na matukar Allah wadai da harin Isra’ila kan cibiyoyin sarrafa nukiliyar Iran da ake amfani da su domin ayyukan zaman lafiya.

Li Song, ya bayyana hakan ne a jiya Juma’a, yayin taron manyan jami’an majalisar gudanarwar hukumar ta IAEA, game da batun hare-haren da Isra’ila ta kaddamar kan cibiyoyin sarrafa nukiliyar Iran. Ya ce, har kullum Sin na mayar da hankali ga zakulo matakan wanzar da zaman lafiya, dangane da batun nukiliyar Iran ta hanyoyin siyasa da diflomasiyya, tana kuma adawa da kakaba takunkumai ba bisa ka’ida ba daga bangare guda. Har ila yau, Sin za ta ci gaba da tattaunawa ta kut-da-kut da dukkanin sassan da batun ya shafa, tare da shawo kan batutuwan gaggawa dake gaban majalisar gudanarwar hukumar ta IAEA. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano
  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran