HausaTv:
2025-05-01@01:10:40 GMT

Nigeria: “Yan Sanda A Jihar Kaduna Sun Kwato Mutane 23 Daga Hannun Barayin Daji

Published: 3rd, February 2025 GMT

Hukumar ‘yan sanda ta jihar Kaduna ta sanar da cewa ta kwato mutane 23 da masu garkuwa da mutane su ka kama a cikin dajin Kajuru da ke karamar hukumar Kajuru.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar ‘yan sandan jihar Kaduna, Mansir Hassan ya sanar a jiya Lahadi cewa sun kwato mutanan ne a ranar 2 ga watan Febrairu, 2025.

Jami’in ‘yan sandan ya ce sun sami nasarar kwato mutanan ne bayan da su ka sami bayanai na sirri akan kai da komowar masu garkuwa da mutanen.

Haka nan kuma Hassan ya ce, an yi taho mu gama ne da masu garkuwa da mutanen a kusa da kauyen Doka dake karamar hukumar ta Kajuru.

Barayin suna kokarin sauya wa mutanen da su ka yi garkuwa da su, wuri ne  a lokacin da ‘yan sandan su ka rutsa da su.

A yayin bata-kashin jami’an tsaro da su ka kunshi ‘yan sanda da kuma sojoji sun kashe barayin masu yawa da kuma tilastawa wadanda su ka saura a raye, janyewa cikin daji.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kwara ta fara yi wa maniyyata rigakafin cututtuka kafin gudanar da aikin Hajji na shekarar 2025.

Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin rigakafin da aka gudanar a harabar hukumar da ke Ilori, shugaban hukumar, Alhaji Abdulsalam Abdulkadir, ya bayyana rigakafin a matsayin wani sharadi da ya zamto wajibi ga dukkan Alhazai bisa umarnin gwamnatin Saudiyya.

Ya ce yin rigakafin yana da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da lafiyar Alhazai a lokacin gudanar da aikin Hajji.

A cewarsa, an shirya shirin rigakafin ne domin hana yaduwar cututtuka da kuma tabbatar da cewa Alhazai sun samu lafiya da kwanciyar hankali yayin aikin Hajjin.

Alhaji Abdulkadir ya bayyana cewa za a fara jigilar rukuni na farko na Alhazai daga jihar zuwa ƙasar Saudiyya ranar 12 ga watan Mayu.

 

Shugaban hukumar ya ƙara da cewa za a kammala aikin rigakafin ne ranar Laraba 30 ga watan Mayu, sannan kuma za a fara raba tufafi da jakunkunan tafiya nan take.

Alhaji Abdulkadir ya yi kira ga maniyyatan da su kammala duk shirye-shiryen lafiyar jiki da na tafiya cikin lokacin da aka kayyade domin samun nasarar aikin Hajjin ba tare da wata tangarda ba.

 

Ali Muhammad Rabi’u

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar