Nigeria: “Yan Sanda A Jihar Kaduna Sun Kwato Mutane 23 Daga Hannun Barayin Daji
Published: 3rd, February 2025 GMT
Hukumar ‘yan sanda ta jihar Kaduna ta sanar da cewa ta kwato mutane 23 da masu garkuwa da mutane su ka kama a cikin dajin Kajuru da ke karamar hukumar Kajuru.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar ‘yan sandan jihar Kaduna, Mansir Hassan ya sanar a jiya Lahadi cewa sun kwato mutanan ne a ranar 2 ga watan Febrairu, 2025.
Jami’in ‘yan sandan ya ce sun sami nasarar kwato mutanan ne bayan da su ka sami bayanai na sirri akan kai da komowar masu garkuwa da mutanen.
Haka nan kuma Hassan ya ce, an yi taho mu gama ne da masu garkuwa da mutanen a kusa da kauyen Doka dake karamar hukumar ta Kajuru.
Barayin suna kokarin sauya wa mutanen da su ka yi garkuwa da su, wuri ne a lokacin da ‘yan sandan su ka rutsa da su.
A yayin bata-kashin jami’an tsaro da su ka kunshi ‘yan sanda da kuma sojoji sun kashe barayin masu yawa da kuma tilastawa wadanda su ka saura a raye, janyewa cikin daji.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bai wa sabon Sarkin Moro’a, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo sandar mulki, a wani biki da aka gudanar a garin Manchok da ke Ƙaramar Hukumar Kaura.
Gwamna Sani, ya bayyana cewa sarakunan gargajiya na taka muhimmiyar rawa wajen zaman lafiya, haɗin kai da kuma ci gaban al’umma.
Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a BinuwaiYa ce gwamnatinsa na bai wa sarakunan gargajiya cikakken goyon baya saboda irin rawar da suke takawa a harkar mulki da ci gaban jama’a.
“Mun jajirce wajen haɗa kan al’umma a faɗin Jihar Kaduna, ba tare da nuna bambanci ba.
“Yanzu Jihar Kaduna ta fi samun tsaro da kwanciyar hankali fiye da da. Wannan nasara ta samuwa ne sakamakon gudunmawar sarakunan gargajiya,” in ji Gwamnan.
Ya kuma buƙaci al’ummar jihar da su zauna lafiya da juna tare da yin aiki tare domin ciyar da jihar gaba.
Haka kuma, ya roƙi sarakunan da su ci gaba da jagorantar al’ummominsu cikin adalci da riƙon amana.
Bikin naɗin sarautar ya samu halartar baƙi daga sassa daban-daban, bayan rasuwar tsohon Sarkin Moro’a, Malam Tagwai Sambo, wanda ya rasu ranar 14 ga watan Yuni 2024.
Tsohon Sarkin ya rasu yana da shekaru 88, bayan mulkin shekaru 58.
Sabon Sarkin, Mai Martaba Isiaku Tagwai Sambo, ya gode wa gwamnati da al’ummar Moro’a bisa amincewar da suka yi masa.
Ya yi alƙawarin mulki cikin gaskiya da riƙon amana tare da bin doka da oda.
“Zamu haɗa kai da majalisar masarauta da kuma ɗaukacin al’umma domin tafiyar da wannan mulki yadda ya kamata,” in ji shi.