Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 12 Cikin Jerin Wadanda Ta Dakatar Da Fitar Musu Da Wasu Kayayyaki Daga Kasar Sin
Published: 10th, April 2025 GMT
Bisa umarnin haramcin, za a dakatar da duk wasu huldodin fitar da hajoji daga kasar Sin zuwa wadannan kamfanoni nan take. Kazalika, a cewar ma’aikatar cinikayyar ta Sin, idan akwai wata bukata ta wajibi, dole ne sassan da za su gudanar da wata hulda mai alaka da hakan su tabbatar sun nemi izni.
Ban da haka kuma, ma’aikatar ta ce kasar ta kara sunayen wasu kamfanonin Amurka 6, cikin jerin sassan da ba za a iya dogaro da su ba.
Ma’aikatar wadda ta bayyana hakan a Larabar nan, ta ce kamfanonin su ne Shield AI, da Sierra Nevada Corporation, da Cyberlux Corporation. Sai kuma Edge Autonomy Operations LLC, da Group W and Hudson Technologies.
Tun daga karfe 12:01 na tsakar ranar gobe Alhamis, takunkumin zai hau kan wadannan kamfanoni, inda za su rasa damarsu ta yin duk wasu huldodin shige da ficen hajoji mai nasaba da kasar Sin, kana an haramta musu zuba duk wani sabon jari a kasar ta Sin. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
An ceto dukkanin mutane 14 ba tare da wani ya ji rauni ba, amma abin baƙin ciki, wani matashi ɗan shekara 27 mai suna Abba daga garin Funtua ya rasa ransa kafin isowar ’yansanda.
A wani lamari da ya faru a ranar 28 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:27 na dare, an sake kiran ’yansanda daga ƙauyen Zagaizagi, inda aka sanar da su cewa wasu ’yan bindiga sum hari tare da sace wasu mutane ƙauyen.
’Yansanda sun isa wajen suka gwabza da ’yan bindigar, kuma sun samu nasarar ceto wasu mutane 14 da kuma ƙwato shanun da aka sace guda biyu.
Amma, mutane biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun rasa rayukansu a harin.
Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da ƙoƙarin kamo ’yan bindigar da suka tsere.
Kwamishinan ’yansandan, CP Bello Shehu, ya yaba wa jami’ansa bisa jarumtaka da suka nuna.
Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai a kan lokaci.
Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp