Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-31@12:38:10 GMT

Ruwa Ya Ci Rayukan Mata Biyu A Kano

Published: 10th, April 2025 GMT

Ruwa Ya Ci Rayukan Mata Biyu A Kano

Mazauna karamar hukumar Gezawa ta Kano sun shiga cikin tashin hankali da makoki sakamakon nutsewar wasu mata biyu a cikin wani tafki.

 

Rahotanni sun nuna cewa matan (an sakaya sunansu) sun gamu da ajalinsu ne a lokacin da suke wanka a kogi bayan sun dawo daga aiki a wata masana’antar sarrafa hibiscus.

 

A cewar jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano Saminu Yusif Abdullahi Gezawa hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa daga ‘yan banga da ke yankin tare da bayyana cewa “Yan uwan ​​matan biyu ne suka kai rahoton lamarin ga dan banga”

 

Ya yi nuni da cewa, nan take aka tura tawagar masu aikin ceto zuwa wurin, inda suka yi nasarar zakulo gawarwakin su a sume, daga bisani jami’an lafiya suka tabbatar da mutuwarsu.

 

Saminu ya bayyana cewa an mika gawarwakin ga wani dan sanda Musa Garba na sashin ‘yan sanda na Gezawa.

 

Ya shawarci jama’a da su daina zuwa kusa da kogi domin gujewa abubuwan da ba a zata ba.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja

Jami’an Hukumar Tsaron Farin Kaya DSS da takwarorinsu na rundunar sojin ƙasa sun kashe aƙalla ’yan ta’adda 45 da ke addabar wasu sassan Jihar Neja.

Bayanai sun ce an kashe ’yan ta’addan ne a ƙauyen Iburu da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro a ranar Juma’ar da ta gabata bayan jami’an DSS sun tattaro bayanan sirri kan harƙallar miyagun a yankin.

Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano Najeriya ta ba wa Habasha kyautar iri da itatuwan cashew 100,000

Majiyoyin tsaro sun ce DSS ta samu bayanan sirri kan wani hari da ’yan ta’addan ke shirin kaiwa ƙauyen Iburu a kan babura, lamarin da sojojin da ke shirin ko-ta-kwana suka tari hanzarinsa.

Ɗaya daga cikin majiyoyin ya shaida cewa an yi musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu, inda aka harbe ’yan ta’adda 45 yayin da jami’an tsaro biyu suka kwanta dama sai kuma huɗu da suka jikkata.

“Mazauna ƙauyukan da lamarin ya shafa sun ce sun ƙidaya aƙalla gawawwakin ’yan ta’adda 40 da kuma gomman babura da aka lalata a yayin musayar wutar.”

Aminiya ta ruwaito cewa wannan tumke ɗamara da ƙara ƙaimi da jami’an tsaron suka yi na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar Kwastam ke bayyana damuwar cewa jami’anta na faɗawa tarkon ’yan ta’adda a yankin.

Ana iya tuna cewa, a watan Afrilun da ya gabata ne Kwanturola Janar na Kwastam, Bashir Adeniyi, ya yi ƙorafin cewa ’yan ta’adda na sheƙe ayarsu a Iyakar Babanna da ke Jihar Neja a ɓangaren da ta yi makwabtaka da Jamhuriyyar Benin.

A wancan lokacin, Adeniyi ya ce jami’ansa sun tsallake rijiya da baya bayan wani kwanton ɓauna da ’yan ta’addan suka yi musu a matsayin ramuwar gayya a sakamakon kame wasu jarkokin man fetur 500 da ake shirin kai musu.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa