Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Published: 19th, April 2025 GMT
· Amfani da intanet cikin tsaro: Wayar da kai tana koya maka yadda za ka yi amfani da wayar salula, kwamfuta, da sauran na’urori cikin kwarewa da tsaro.
· Sanin sirrinka da darajarsa: Mutum zai fi kulawa da bayanansa na sirri da yadda za su iya amfani da su wajen cutar da shi idan ya samu ilimi.
Abubuwan Da Ya Kamata Ka Kula Da Su
1.
2. Kar ka rika danna kowanne link da ba ka tabbatar da amincinsa ba.
3. Rika sabunta (update) wayarka ko kwamfutarka domin gyara kura-kurai na tsaro.
4. Amfani da kalmar sirri (password) mai karfi da bambanta lambobi da haruffa.
5. Kada ka bayyana bayanan banki, katin ATM, ko lambarka ta sirri a dandalin sada zumunta.
Kammalawa
Wayar da kai kan cyber ba wai na ‘yan kasuwa da ma’aikata bane kadai ba. Kowa na bukatar hakan – dalibi, mai sayar da kaya, iyaye da yara. Mu dauki mataki tun yanzu domin kare kanmu da iyalanmu daga barazanar cyber.
Ku ci gaba da kasancewa da mu domin koyon dabarun tsare kai a intanet. Cyber Awareness shine matakin farko zuwa Cyber Security!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Barazana
এছাড়াও পড়ুন:
An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
A yayin da ake tsaka da bikin Ranar Dimokradiyya a Najeriya, al’ummar jihar Gombe sun wayi gari da sabuwar dokar takaita zirga-zirgar babura daga ƙarfe 7:00 na yamma zuwa ƙarfe 6:00 na safe a duk faɗin jihar.
Sanarwar da ta fito ne daga hannun Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda ta jihar, DSP Buhari Abdullahi, ranar Alhamis, a madadin kwamishinan ’yan sandan jihar Bello Yahaya.
Sanarwar ta ce an kafa dokar ne don rage ayyukan ta’addanci a fadin jihar.
Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a FilatoKafa dokar na zuwa ne kwana uku bayan wasu matasa da ba a tantance su wane ne ba suka kashe wani magidanci mai suna Ahmad Aliyu, wanda aka fi sani da Amadi Kasiran, a unguwar Hammadu Kafi da ke Gombe, a daren Lahadi.
Sanarwar ta ƙara da cewa duk wanda aka kama ya karya dokar zai fuskanci hukunci mai tsauri, ciki har da gurfanar da shi a gaban kotu.
Kazalika, sanarwar ta ce dokar ta haramta ɗaukar mutum fiye da ɗaya a kan babur domin rage matsalar rashin tsaro a jihar.
“Dokar hana hawa babur da goyon biyu ta fara aiki ne daga yau, Alhamis, ranar bikin Dimokradiyya, har sai wani lokaci da ba a kayyade ba,” in ji Kakakin ’yan sandan.
Rundunar ’yan sandan ta ce an ɗauki wannan mataki ne don magance matsalar bata-gari na ‘’yan kalare’ da sauran ayyukan ta’addanci.
A lokacin da wakilinmu ya kai ziyara kwaryar birnin Gombe, filin wasa na Pantami ya kasance a rufe ba tare da alamar wani biki ba.
Sai dai ya gane wa idanunsa cewa an jibge jami’an tsaro a sassa daban-daban, ciki har da ’yan sanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da kuma ’yan banga.
Wannan sabuwar doka ta ja hankalin mutane da dama a jihar, musamman mazauna yankunan da aka fi samun matsalar tsaro.
Sai dai wasu na gani za ta kara jefa jihar cikin kuncin talauci sakamakon rufe shaguna da kasuwanni da wuri saboda rashin abun hawa wanda dama can baburan aka fi hawa saboda tsadar rayuwa.