Aminiya:
2025-05-31@20:54:32 GMT

An buɗe wa jami’an NDLEA wuta a Abuja

Published: 19th, April 2025 GMT

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) sun tsallake rijiya da baya da raunukan harbin bindiga bayan da ɓata-gari suka buɗe musu wuta a lokacin da suka kama miyagun ƙwayoyi a Yankin Banban Birnin Tarayya.

Mutum uku daga cikin jami’an sun samu raunuka an harbi, ɗaya a haƙari, biyu a gadon baya da kafafunsu, a yayin harin da aka kai musu a unguwar Jahi, bayan sun kama wasu miyagun ƙwayoyi a ranar Alhamis.

Kakakin NDLEA na ƙasa, Femi Babafemi, ya bayyana cewa an kwantar da jami’an guda uku a asibiti saboda raunukan harbin bindiga da suka samu.

“Lamarin ya faru ne a lokacin da tawagar jami’an NDLEA, bisa bayanan sirri, suka kai samame wani kwangon gini a yankin NNPC da ke unguwar Jahi inda aka ƙwato kwalaben codeine guda 74, codeine ta ruwa lita 10, gram 48 na tramadol mai milligram 225, da kilogiram 4.9 na skunk, wani nau’in tabar wiwi, da kuma wayoyin android guda biyar.

’Yan sanda sun ceto ɗalibai 10 sun lashe ɗan bindiga a Edo Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayi

“Yayin da tawagar NDLEA ke hanyarsu ta fita daga wurin kuma an kai musu harin bindiga,” in ji Babafemi a cikin sanarwar da ya fitar washegari da daddare.

Babafemi ya ce, an fara ba da kulawar gaggawa ga jami’an da suka ji rauni a asibitin ’yan sanda da ke Garki Area 1 kafin a mayar da su Babban Asibitin Abuja domin ƙarin kulawa.

Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Mohamed Buba Marwa (Mai Ritaya), ya yaba wa ma’aikatan asibitin ’yan sanda bisa ga agajin gaggawar da suka bayar.

Ya kuma gode wa Shugaban Asibitin Ƙasa, wanda shi da kansa ya tuntube shi domin ya kula da jinyar jami’an da suka ji rauni.

Shugaban NDLEA, wanda ke Kano a kan ayyukan hukuma, ya kuma yi magana ta waya da jami’an da suka ji rauni domin yi musu fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

Ya ba su tabbacin cewa hukumar za ta yi amfani da duk wata hanya da take da ita kuma za ta yi aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin gano waɗanda ke da alhakin kai musu harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ƙwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Za a ɗauke ruwan famfo na tsawon mako 2 a Abuja 

Mazauna Babban Birnin Tarayya za su fuskanci katsewar ruwan sha na tsawon makonni biyu, kamar yadda Hukumar Kula da Ruwa ta yankin ta sanar.

Rashin ruwan, wanda ya fara ranar Juma’a, 30 ga Mayu, ana sa ran za ta ci gaba har zuwa ranar Juma’a, 13 ga Yuni.

Matsalar ta samo asali ne daga ayyukan gyare-gyare da ake yi a tashoshin tace ruwa na madatsar ruwa ta Lower Usuma Dam.

A cewar sanarwar da hukumar ta fitar, gyare-gyaren sun shafi muhimmin aikin haɗa kayan aikin lantarki da injiniya, wanda babban bangare ne na aikin inganta matatar.

Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Borno

Wannan aiki ya tilasta dakatar da rarraba ruwa na ɗan lokaci zuwa tsakiyar birnin da kuma yankunan wajenta.

Hukumar ta shawarci jama’a da su tanadi isasshen ruwa da zai ishe su tsawon lokacin, sa’annan su nemi wasu hanyoyin samun ruwa don biyan bukatunsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Masu Shiga Tsakani Amurkawa Su Gamsar da Ita Za’a Dakatar Da Yaki A Gaza
  • Za a ɗauke ruwan famfo na tsawon mako 2 a Abuja 
  • Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa
  • An gano gawar direba a cikin mota a Bayelsa
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza
  • Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
  • An kama mutum 41 da ake zargi da kisan DPO a Kano
  • NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
  • ’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna