Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran
Published: 19th, April 2025 GMT
Iran da Amurka za su shiga zagaye na biyu na tattauna batun taƙaita shirin nukiliyar Tehran a yau Asabar.
Masu shiga tsakani za su haɗu a birnin Roma bayan zagayen farko na tattaunawar da aka yi a makon jiya a Oman.
Ministan harkokin wajen Iran ya ce za a iya cimma yarjejeniya idan Amurka ba ta gabatar da wasu sharuɗa da Tehran ba za ta yi bi ba.
Shugaba Trump ya sha yin barazanar yin amfani da ƙarfin soji idan Iran ta ƙi amincewa da wata yarjejeniya.
Ana ta samun bayanan da suka ci karo da juna game da abubuwan da Washington za ta gabatar da yarjejeniyar.
Tehran ta yi bayani ƙarara cewa ba za ta taɓa yadda da batun rushe shirinta na nukiliya baki ɗaya ba.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Iran
এছাড়াও পড়ুন:
Miliyoyin Mutane Sun Gudanar Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”
Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.
A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.