Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran
Published: 19th, April 2025 GMT
Iran da Amurka za su shiga zagaye na biyu na tattauna batun taƙaita shirin nukiliyar Tehran a yau Asabar.
Masu shiga tsakani za su haɗu a birnin Roma bayan zagayen farko na tattaunawar da aka yi a makon jiya a Oman.
Ministan harkokin wajen Iran ya ce za a iya cimma yarjejeniya idan Amurka ba ta gabatar da wasu sharuɗa da Tehran ba za ta yi bi ba.
Shugaba Trump ya sha yin barazanar yin amfani da ƙarfin soji idan Iran ta ƙi amincewa da wata yarjejeniya.
Ana ta samun bayanan da suka ci karo da juna game da abubuwan da Washington za ta gabatar da yarjejeniyar.
Tehran ta yi bayani ƙarara cewa ba za ta taɓa yadda da batun rushe shirinta na nukiliya baki ɗaya ba.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Iran
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja
Jami’an Hukumar Tsaron Farin Kaya DSS da takwarorinsu na rundunar sojin ƙasa sun kashe aƙalla ’yan ta’adda 45 da ke addabar wasu sassan Jihar Neja.
Bayanai sun ce an kashe ’yan ta’addan ne a ƙauyen Iburu da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro a ranar Juma’ar da ta gabata bayan jami’an DSS sun tattaro bayanan sirri kan harƙallar miyagun a yankin.
Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano Najeriya ta ba wa Habasha kyautar iri da itatuwan cashew 100,000Majiyoyin tsaro sun ce DSS ta samu bayanan sirri kan wani hari da ’yan ta’addan ke shirin kaiwa ƙauyen Iburu a kan babura, lamarin da sojojin da ke shirin ko-ta-kwana suka tari hanzarinsa.
Ɗaya daga cikin majiyoyin ya shaida cewa an yi musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu, inda aka harbe ’yan ta’adda 45 yayin da jami’an tsaro biyu suka kwanta dama sai kuma huɗu da suka jikkata.
“Mazauna ƙauyukan da lamarin ya shafa sun ce sun ƙidaya aƙalla gawawwakin ’yan ta’adda 40 da kuma gomman babura da aka lalata a yayin musayar wutar.”
Aminiya ta ruwaito cewa wannan tumke ɗamara da ƙara ƙaimi da jami’an tsaron suka yi na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar Kwastam ke bayyana damuwar cewa jami’anta na faɗawa tarkon ’yan ta’adda a yankin.
Ana iya tuna cewa, a watan Afrilun da ya gabata ne Kwanturola Janar na Kwastam, Bashir Adeniyi, ya yi ƙorafin cewa ’yan ta’adda na sheƙe ayarsu a Iyakar Babanna da ke Jihar Neja a ɓangaren da ta yi makwabtaka da Jamhuriyyar Benin.
A wancan lokacin, Adeniyi ya ce jami’ansa sun tsallake rijiya da baya bayan wani kwanton ɓauna da ’yan ta’addan suka yi musu a matsayin ramuwar gayya a sakamakon kame wasu jarkokin man fetur 500 da ake shirin kai musu.