HausaTv:
2025-07-31@01:05:45 GMT

Iran ta yi tir da kakkausar murya da harin Amurka kan tashar mai ta Yemen

Published: 19th, April 2025 GMT

Iran ta yi tir da Allah wadai da kakkausan lafazi da harin Amurka na baya baya nan kan tashar mai ta kasar Yemen, wanda ya yi sanadin mutuwar gomman mutane tare da lalata dukiya mai yawa.

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghai, ya kira harin da Amurka ta kai a matsayin keta kundin tsarin mulkin MDD da kuma dokokin kasa da kasa karara.

Misata Baghai ya ce : “Hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen, a matsayin cikakken goyon bayanta ga mamaya da kuma kisan kiyashin da gwamnatin sahyoniya ta ke yi a yankunan Falasdinawa, ya sanya Amurka ta zama mai hannu dumu-dumu a kan laifukan da Isra’ila ke aikatawa a Falastinu da kuma yankin.”

Akalla mutane 80 ne suka rasa rayukansu tare da jikkata wasu 150 a harin da Amurka ta kai kan tashar jiragen ruwan ta Ras Issa a Yemen.

Wannan dai shi ne hari mafi muni tun bayan fara farmakin na Amurka a Yemen yau sama da watanni 15.

Sojojin Amurka sun sanar da cewa sun kai hari tare da lalata tashar jiragen ruwa na Ras Issa da ke lardin Hodeida a ranar Alhamis da nufin hana ‘yan Houthi kudaden shiga da suke amfani da su wajen daukar nauyin ayyukansu da kuma ta’addanci a yankin.

Saidai ‘yan Houtsis, sun ce ‘’Ras Issa “tashar ruwa ce ta farar hula inda jiragen ruwa da ke dauke da mai da dizal da iskar gas ke isa domin raba mai ga dukkan yankunan Yemen.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da aniyar ta ta bunƙasa harkar kiwon dabbobi a Nijeriya a matsayin wata muhimmiyar hanya ta magance rikice-rikicen da ke tsakanin manoma da makiyaya, tare da amfani da damar tattalin arzikin da ke cikin ɓangaren.

Ɗaya daga cikin Shugabannin Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Harkar Kiwo, Farfesa Attahiru Jega, shi ne ya bayyana hakan a wurin taron tattaunawa tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa, wanda Gidauniyar Sa Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna, a ranar Laraba.

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

Jega ya bayyana cewa sabuwar Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo tana ɗaya daga cikin ginshiƙan da ke cikin shirin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na sauya fasalin ɓangaren kiwon dabbobi.

Ya jaddada cewa ana aiwatar da hangen nesa na Shugaban Ƙasa ba tare da son rai na siyasa ba, tare da mayar da hankali kan haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, al’ummomin makiyaya da sauran muhimman masu ruwa da tsaki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ