HausaTv:
2025-11-02@03:37:28 GMT

Iran ta yi tir da kakkausar murya da harin Amurka kan tashar mai ta Yemen

Published: 19th, April 2025 GMT

Iran ta yi tir da Allah wadai da kakkausan lafazi da harin Amurka na baya baya nan kan tashar mai ta kasar Yemen, wanda ya yi sanadin mutuwar gomman mutane tare da lalata dukiya mai yawa.

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghai, ya kira harin da Amurka ta kai a matsayin keta kundin tsarin mulkin MDD da kuma dokokin kasa da kasa karara.

Misata Baghai ya ce : “Hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen, a matsayin cikakken goyon bayanta ga mamaya da kuma kisan kiyashin da gwamnatin sahyoniya ta ke yi a yankunan Falasdinawa, ya sanya Amurka ta zama mai hannu dumu-dumu a kan laifukan da Isra’ila ke aikatawa a Falastinu da kuma yankin.”

Akalla mutane 80 ne suka rasa rayukansu tare da jikkata wasu 150 a harin da Amurka ta kai kan tashar jiragen ruwan ta Ras Issa a Yemen.

Wannan dai shi ne hari mafi muni tun bayan fara farmakin na Amurka a Yemen yau sama da watanni 15.

Sojojin Amurka sun sanar da cewa sun kai hari tare da lalata tashar jiragen ruwa na Ras Issa da ke lardin Hodeida a ranar Alhamis da nufin hana ‘yan Houthi kudaden shiga da suke amfani da su wajen daukar nauyin ayyukansu da kuma ta’addanci a yankin.

Saidai ‘yan Houtsis, sun ce ‘’Ras Issa “tashar ruwa ce ta farar hula inda jiragen ruwa da ke dauke da mai da dizal da iskar gas ke isa domin raba mai ga dukkan yankunan Yemen.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta

Iran ta yi ikirarin cewa Darakta Janar na Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Duniya (IAEA), Rafael Grossi, ya “san”sarai da cewa shirin nukiliyar kasar na lumana ne, don haka ya kamata ya guji yin “kalamai marasa tushe” kan lamarin.

A wata hira da ya yi da tashar Al Jazeera, kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Esmail Baghai ya bayyana cewa kalaman da Rafael Grossi ya yi a baya sun share fagen ayyukan ta’addanci da Amurka da gwamnatin Isra’ila suka yi wa Iran a watan Yunin da ya gabata.

Ya kamata Darakta Janar na IAEA ya guji yin kalamai marasa tushe game da shirin nukiliya na Iran, in ji shi.

Rafael Grossi ya bayyana a ranar Laraba cewa IAEA ta gano kwanan nan da sake dawowa da ayyuka a wuraren nukiliya na Iran,” bayan ya amince cewa kasar ba ta nuna alamun kara wadatar da uranium ba.

A cikin wani rahoto na sirri da aka gabatar wa Kwamitin Gwamnonin IAEA a ranar 31 ga Mayu, 2025, Babban Daraktan IAEA ya yi iƙirarin cewa “Iran ta gaza bayyana ayyukanta na nukiliya a wurare uku da ba a bayyana ba” kuma ta bayyana damuwa game da tarin sinadarin uranium da ta wadatar zuwa kashi 60%.

A cewar jami’an Iran, rahoton Grossi game da shirin nukiliya na Tehran ya share fagen kai hari ga Isra’ila kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

A karshen watan Yuni ne, Majalisar Tsaron Iran ta amince da wani kudiri da majalisar dokokin kasar ta zartar wanda ya dakatar da haɗin gwiwa da hukumar ta IAEA.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta
  • Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri
  • Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai