Aminiya:
2025-07-31@13:46:47 GMT

Fasinja ya yi ƙoƙarin buɗe ƙofar jirgi a sararin samaniya

Published: 6th, April 2025 GMT

Jirgin da ke ɗauke da mutane sama da 200 daga Bali a ƙasar Indonesia zuwa Ostireliya, ya yi juyawar dole bayan wani fasinja ya yi yunƙurin buɗe ƙofarsa yayin da jirgin kamfanin Jetstar ke shawagi a tekun Indiya.

“Mun samu wani jirgin sama ya koma Denpasar (filin jirgin sama na Bali) a daren Talata bayan wani ruɗaɗen fasinja ya yi yunƙurin buɗe ɗaya daga cikin kofofin jirgin kuma ya ci zarafin ma’aikatanmu,” a cewar wata sanarwa da kamfanin jirgin sama ya fitar game da lamarin a daren Litinin, 31 ga Maris.

Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya Tsohon Gwamnan Oyo Olunloyo ya riga mu gidan gaskiya

Hukumomin yankin Bali ne suka fitar da fasinjan daga cikin jirgin.

A wani bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta, wata mata a bayan jirgin ta yi nasarar daga hannun kofar kafin sakon gargadi ya sanar da ma’aikatan jirgin, in ji kyaftin a amsa kuwwa jirgin (sifika).

Bayanai daga shafin sa ido na jirgin na Flightradar24 sun nuna cewa jirgin ya bi ta kan tekun Indiya kimanin sa’a guda a cikin jirgin.

Jetstar bai bayyana ainihin adadin fasinjoji da ma’aikatan jirgin da ke cikin jirgin da ya taso daga Bali zuwa Melbourne ba.

A cikin sanarwar da kamfanin ya fitar ta ce “Tsaro da walwalar abokan cinikinmu da ma’aikatan jirgin shi ne babban abin fifikonmu kuma muna gode musu kan yadda suka amsa lamarin.

“Ba za a taɓa yarda da irin wannan dabi’ar ba, ba za a amince da ita ba a cikin jirginmu.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sawagi

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan

Alkalin alkalan JMI Gholamhussain Muhsen Ejei, ya bayyana cewa, babu shakka gwamnatin kasar Amurka tana da hannu a hare-haren da ake dangantawa da kungiyar yan ta’adda ta Jaishul Zulm da ya faru a cikin wani kotu a garin Zahidan na lardin sistan Baluchistan a cikin yan kwanakin da suka gabata.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto alkalin alkalan yana fadar haka a lokacinda ya kai ziyara a gaisuwar wadanda abin ya shafa. Ya kuma bukaci mataimakinsa ya gabatar da dukkan bukatun da wadanda abin ya shafa suka gabatar.

A cikin maganar sa alkalin alkalan ya bayyana cewa, an halaka mutane uku a musayar wuta da yan ta’addan a kusa da kotun. Sannan JMI ta samar da shahidai 6 sannan wasu 22 suka ji rauni.

Yankin Sistan Baluchistan dai ya dade yana fama da hare-hare na wannan kungiyar, kuma tana da sansani a cikin kasar Pakistan wacce take makobtaka da kasar a kudu maso gabacin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami
  • An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata