HausaTv:
2025-12-07@12:20:06 GMT

Isra’ila ta kaddamar da hare-hare ta kasa a tsakiya da kudancin zirin Gaza

Published: 19th, March 2025 GMT

Rundunar sojin Isra’ila ta sanar a ranar Larabar nan da cewa, ta kaddamar da hare-hare ta kasa a tsakiya da kudancin zirin Gaza, biyo bayan hare-haren wuce gona da iri kan yankin Falasdinu.

Sanarwar ta bayyana cewa, sojojin sun karbe iko tare da fadada shi zuwa tsakiyar hanyar Netzarim, da nufin fadada yankin tsaro da samar da wani bangare na raba tsakanin arewaci da kudancin Gaza.

A halin da ake ciki kuma, ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya yi gargadin karshe ga Falasdinawa a zirin Gaza, inda ya bukaci da su sako Isra’ilawa da suke garkuwa da su, su kuma kawar da kungiyar Hamas, a cewar wata sanarwa daga ofishinsa.

“Idan ba a sako dukkan mutanen Isra’ila da aka yi garkuwa da su ba, kuma ba a kawar da Hamas gaba daya daga Gaza ba, Isra’ila za ta dauki matakan da ba a taba ganin irinta ba inji shi.

“Muna ba ku shawarar ku bi shawarar shugaban Amurka: ku saki mutanen da aka yi garkuwa da su, ku kawar da Hamas,” in ji Katz a wani faifan bidiyo na yaren Hebrew da ofishinsa ya fitar.

Firayi inistan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce ya umurci sojojin da su dauki ” mataki” kan Hamas a Gaza, yana mai zargin kungiyar da kin sakin fursunoni da rashin amincewa da shawarwarin Isra’ila kan tsagaita bude wuta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21

Kungiyar ‘yan wasan  ” Taekwondo” Iran dake kasa a shekaru 21 sun zama gwarazan duniya da aka yi a birnin Nairobi, bayan da su ka sami zinariya 3 da azurfa 1 sai kuma tagulla biyu.

Kamfanin dillancin labarun “Irna” ya nakalto cewa; a jiya Asabar ne aka kawo karshe gasar wasan na ” Taekwondo” wanda ya sami halartar ‘yan wasa 452 daga kasashe 75.

A ranar ta karshe ta wasan, dan wasan Iran Muhammad Aizadeh, ya sami azurfa, sai kuma wani dan wasan “Matin Rizayi wanda ya sami tagulla.

Wadanda su ka sami zinariya kuwa su ne Abul Fadl Zandi, da Radin Zinalu sai kuma Amir Riza Gulami.

 Kasar Turkiya ta zo ta biyu da ta sami zinariya biyu da azurfa daya, sai kasar Khazakistan wacce ta zo ta uku da ta sami zinariya biyu da tagulla daya. Kasar da ta biyo bayanta ita ce Masar da da Bulgaria sai India.

A fagen mata kuwa, Iraniyawa 6 ne su ka sami kyautuka, inda kungiyarsu ta zo ta hudu.

An kuma zabi Majid Afkali na Iran a matsayin mai bayar da horo na daya, sai kuma Abul Fadl Zandi wanda aka zaba a matsayin dan wasa na farko.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi December 7, 2025  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada December 7, 2025 Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurumin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi December 6, 2025   Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba December 6, 2025 Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika December 6, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi December 6, 2025 Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026 December 6, 2025 Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza December 6, 2025 Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
  • Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya
  • Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21
  • Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurmin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi
  •   Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • Afirka ta Kudu Za Ta Dauki Hutu Daga Halartar Tarukan G20 A Karkashin Shugabancin Trump
  •  Jiragen Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon
  • An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya