HausaTv:
2025-12-12@19:55:49 GMT

Isra’ila ta kaddamar da hare-hare ta kasa a tsakiya da kudancin zirin Gaza

Published: 19th, March 2025 GMT

Rundunar sojin Isra’ila ta sanar a ranar Larabar nan da cewa, ta kaddamar da hare-hare ta kasa a tsakiya da kudancin zirin Gaza, biyo bayan hare-haren wuce gona da iri kan yankin Falasdinu.

Sanarwar ta bayyana cewa, sojojin sun karbe iko tare da fadada shi zuwa tsakiyar hanyar Netzarim, da nufin fadada yankin tsaro da samar da wani bangare na raba tsakanin arewaci da kudancin Gaza.

A halin da ake ciki kuma, ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya yi gargadin karshe ga Falasdinawa a zirin Gaza, inda ya bukaci da su sako Isra’ilawa da suke garkuwa da su, su kuma kawar da kungiyar Hamas, a cewar wata sanarwa daga ofishinsa.

“Idan ba a sako dukkan mutanen Isra’ila da aka yi garkuwa da su ba, kuma ba a kawar da Hamas gaba daya daga Gaza ba, Isra’ila za ta dauki matakan da ba a taba ganin irinta ba inji shi.

“Muna ba ku shawarar ku bi shawarar shugaban Amurka: ku saki mutanen da aka yi garkuwa da su, ku kawar da Hamas,” in ji Katz a wani faifan bidiyo na yaren Hebrew da ofishinsa ya fitar.

Firayi inistan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce ya umurci sojojin da su dauki ” mataki” kan Hamas a Gaza, yana mai zargin kungiyar da kin sakin fursunoni da rashin amincewa da shawarwarin Isra’ila kan tsagaita bude wuta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’

Wani mazaunin Kano, Namadi Bawa, ya bayyana yadda ya shiga cikin daji a Jihar Zamfara domin kai kudin fansa ga ’yan bindiga da suka sace ɗan uwansa, inda ya tarar da su cikin mawuyacin hali na rashin lafiya, kafin daga bisani ya samu ya kubutar da shi. A tattaunawar mutumin da Aminiya, y ace an sace ɗan uwan nasa ne a Gusau babban birnin jihar Zamfara, a kan hanyarsa ta dawowa daga Sakkwato.A cewar Namadi, ɗan uwansa ya ci karo da shingen da ya yi kama da na jami’an tsaro a hanya, sai dai daga baya aka gano ’yan bindiga ne suka yi masa kwantan bauna tare da wasu fasinjoji.

“Sun kira ni suka tambaya ko na san ɗan uwana, na ce eh. Suka ce sun sace shi kuma yana hannunsu. A lokacin kwana ɗaya kenan da sace shi,” in ji Namadi.

Cinikin kuɗin fansa da tafiya daji domin kai musu

Ya ce masu garkuwar sun fara neman kuɗin fansa har Naira miliyan 16, amma bayan tattaunawa aka rage zuwa miliyan bakwai.

Namadi ya ce masu garkuwar sun yi gargaɗin cewa ba za su lamunci rage wani abu daga adadin kudin da aka yi cinikin ba, suna gargaɗin cewa muddin suka ƙirga kuɗin suka ga ba su cika ba, za a ga ba daidai ba.

“Sun ja hankali cewa kada a rage ko ƙwandala a ciki, idan aka rage za a ga ba daidai ba,” in ji shi.

Namadi ya bayyana yadda ya je da kansa ya kai kudin cikin daji.

A cewarsa, an umurce shi ya tsaya a wani ƙauye kafin daga bisani a nuna masa hanyar shiga. Daga bisani aka ba shi wata riga ya saka kafin ya isa wurin da aka karɓi kudin.

“Na zaci za su ƙirga kudin, amma sai suka tattaka su da ƙafa, suka ce sun cika. Bayan haka suka ce na gangaro daga kan dutsen da suka kai ni. Na yi ta kallo ko zan ga ɗan uwana, amma daga baya ne suka nuna min shi tare da wasu da aka sace, duk suna kwance cikin yanayin rashin lafiya,” in ji shi.

Yanayin dajin da masu garkuwar

Namadi ya ce yanayin da ya tarar da su ya nuna suna fama da cutar kwalara, inda aka ajiye su a bukka a tsakiyar dajin da ba motar da za ta iya shiga sai babur.

“Na san idan a wannan yanayin ne, ba za su yi dogon zango ba. Ta su za ta kare,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ɗan uwansa da sauran da aka sace sun shiga mawuyacin hali, inda dole ne aka kai ɗan uwansa asibiti bayan an karɓo shi saboda yanayin da aka same shi.

Namadi ya kuma ce duk da fargaba da tashin hankalin da ya shiga, addu’a ce ta taimaka masa ya dawo gida lafiya.

“Mu ci gaba da addu’a saboda tana da tasiri a kan mutanen nan. Insha Allahu Allah zai kawo ƙarshen su,” in ji shi.

Cin karo da wasu masu garkuwar a hanyar dawowa

Bayan ya karɓo ɗan uwansa, Namadi ya ce a hanyarsa ta fita daga dajin ya sake cin karo da ’yan bindigar sun kamo wasu mutanen, suna kaɗa su zuwa cikin daji.

“Sun ba ni shawara kada na bi ta inda na zo, saboda akwai ƙungiyoyin masu garkuwa da dama a yankin waɗanda ba sa ga maciji da juna da za su iya sake kama mu,” in ji shi.

Daga nan sai ya ce duk da muggan makaman da ’yan bindigar ke da su, ba su fi ƙarfin gwamnati ba.

Ya yi kira ga gwamnati da ta ƙara ƙoƙari wajen kawar da ’yan bindiga a yankin, tare da fatan addu’ar jama’a za ta taimaka wajen kawo ƙarshen matsalar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • ‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahadi A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran
  • Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD
  • Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Hare-Hare Kan Sojojin Pakistan Sun Kuma Kashe 6 Daga Cikinsu