Kimani makonni biyu Kenan jumhuriyar Najer tana fama da karancin man fetur a gidajen man kasar, wanda ya rage zirga-zirgan ababen hawa a duk fadin kasar har da Yemai babban birnin kasar, har’ila yau ya shafi harkokin tattalin arzikin kasar.

Shafin yana labarai na yanar gizo IR News, ya bayyana cewa bayan da gwamnatin sojojin kasar ta kasa magance matsalar a cikin gida, ta tura wata tawaga karkashin jagorancin Ministan man fetur na kasar zuwa tarayyar Najeriya tare da bukatar ta aiko mata tataccen man fetur don magance matsalar.

Labarin ya kara da cewa, gwamnatin tarayyar Najeriya dai tuni ta amince da bukatar, tare da bada umurnin a aikawa Jumhuriyar ta Niger tankunan man fetur har 300.

Wasu wadanda suka san al-amura a Jumhuriyar ta Niger sun bayyana cewa matsalar ta taso ne bayan da gwamnatin sojojin kasar suka sami matsala da kamfanin kasar China wanda yake haka da tashen man fetur a matatan mai ta Soraz, wanda ya kai da sojojin suka bukaci mutanen china su bar kasar.

JMI tana haka da sarrafa danyen man fetur tun shekara ta 2011, amma matsala tsakanin gwamnatin sojojin kasar da kasar China ta sa sun kasa samar da man da zai water da kasar, ballanta na a yi maganar ganga 100,000 da kasar take son fara saida shi ga kasashen waje, ta hanyar bututun mai wanda zai bi ta kasar Benin zuwa kasuwannin duniya.

Juye-juyen mulkin da aka yi a yankin Sahel dai ya sa Jumhuriyar Niger bata jituwa da kasashen kungiyar ECoWAW. Wacce Najeriya take jagoranta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Duk Tare Da Amurkawa Sun Ce Za’a Yi

Kakakin gwamnatin JMI ta bayyana cewa a dai-dai lokacinda Amurka ta kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliyar kasar , babu wata tattaunawa da Amurka nan kusa, duk tare da cewa Amurkawan sun bayyana cewa za’a ci gaba da shi.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kakakin gwamnatin kasar Iran Malama Fatimah Muhajirani tana fadar haka a jiya Talata, ta kuma kara da cewa, babu wata rana da aka sanya na tattaunawa da Amurka kuma mai yuwa babu wata tattaunawa da ita nan kusa.

Fatima tana maida martani ne ga wata sanarwan da gwamnatin kasar Amurka ta bayara na, na cewa nan kusa zasu sake farfado da tattaunawa da JMI.  Tehran dai ta bayyana cewa bata bukatar wani tattaunawa da Amurka kuma bayan hare-haren da ta kai kan cibiyoyin nukliyar kasar guda 3 a dai dai lokacinda HKI ta fadawa kasar da yaki tare da amincewarta.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata
  • JMI Ta Bukaci Kungiyar Majalisun Dokoki Ta Duniya Su Kori HKI Daga Cikinta
  • Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Duk Tare Da Amurkawa Sun Ce Za’a Yi
  • Wargajewar HKI Ba Makawa Inji Wani Janar Daga Sojojin JMI
  • Kotu za ta duba yiwuwar ba da belin Tukur Mamu a ranar 22 ga watan Yuli
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya
  • Laftanar Kanar Shikarci: Sojojin Iran Suna Cikin Shirin Ko-Ta-Kwana Fiye Da Kowane Lokaci
  • An Kashe ‘Yan Kungiyar Shabab 19  A Kasar Somaliya
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya
  •  HKI:Har Yanzu Matatar Man Fetur Ta Haifa Ba Ta Koma Aiki Ba