Jumhuriyar Najer Ta Bukaci Tarayyar Najeriya Ta Taimaka Don Warware Matsalar Karancin Makamashi A Kasar
Published: 15th, March 2025 GMT
Kimani makonni biyu Kenan jumhuriyar Najer tana fama da karancin man fetur a gidajen man kasar, wanda ya rage zirga-zirgan ababen hawa a duk fadin kasar har da Yemai babban birnin kasar, har’ila yau ya shafi harkokin tattalin arzikin kasar.
Shafin yana labarai na yanar gizo IR News, ya bayyana cewa bayan da gwamnatin sojojin kasar ta kasa magance matsalar a cikin gida, ta tura wata tawaga karkashin jagorancin Ministan man fetur na kasar zuwa tarayyar Najeriya tare da bukatar ta aiko mata tataccen man fetur don magance matsalar.
Labarin ya kara da cewa, gwamnatin tarayyar Najeriya dai tuni ta amince da bukatar, tare da bada umurnin a aikawa Jumhuriyar ta Niger tankunan man fetur har 300.
Wasu wadanda suka san al-amura a Jumhuriyar ta Niger sun bayyana cewa matsalar ta taso ne bayan da gwamnatin sojojin kasar suka sami matsala da kamfanin kasar China wanda yake haka da tashen man fetur a matatan mai ta Soraz, wanda ya kai da sojojin suka bukaci mutanen china su bar kasar.
JMI tana haka da sarrafa danyen man fetur tun shekara ta 2011, amma matsala tsakanin gwamnatin sojojin kasar da kasar China ta sa sun kasa samar da man da zai water da kasar, ballanta na a yi maganar ganga 100,000 da kasar take son fara saida shi ga kasashen waje, ta hanyar bututun mai wanda zai bi ta kasar Benin zuwa kasuwannin duniya.
Juye-juyen mulkin da aka yi a yankin Sahel dai ya sa Jumhuriyar Niger bata jituwa da kasashen kungiyar ECoWAW. Wacce Najeriya take jagoranta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
Wani abun lura ma a nan shi ne yadda a matsayinta na kasa mai tasowa ta farko a tarihin duniya da ta cimma nasarar samun wadata cikin lumana, Sin ta samar da wata taswira mai inganci, wadda sauran kasashe masu tasowa za su iya bi domin raya kansu cikin lumana, kuma karkashin hakan ne take ta fitar da shawarwari na ingiza ci gaban duniya bi da bi, irinsu shawarar raya jagorancin duniya da kasar ta gabatar a baya bayan nan. Shawarar da masharhanta da yawa ke ganin na da ma’anar gaske, wajen ingiza adalci, da daidaito a tsarin cudanyar mabanbantan sassan duniya.
A gani na tun da har kasar Sin ta kai ga gina tsari mai gamsarwa na raya kai bisa salon musamman mafi dacewa da yanayinta, wanda kuma yake ta kara samun karbuwa tsakanin kasashen duniya, a halin yanzu, kasar na kan wani matsayi na rarraba kwarewarta tare da sauran abokan tafiya, musamman kasashe masu tasowa. Wanda hakan kyakkyawan misali ne da dukkanin wata kasa a duniyan nan za ta iya lura da shi, yayin da take kokarin bunkasa kanta gwargwadon yanayin da take ciki.
Tabbas, ci gaban kasar Sin mai ban mamaki ya nunawa duniya cewa, kowace kasa na iya samun ci gaba ba tare da murdiya, muzgunawa wasu sassa, ko nuna karfin iko na siyasa ko tattalin arziki ba, maimakon hakan kasar Sin ta nunawa duniya cewa abu ne mai yiwuwa, a samu ci gaba bisa hadin gwiwar cimma moriya tare, ta yadda za a gudu tare a kuma tsira tare.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA