A kwanan nan ne aka fitar da motar daukar mara lafiya ta farko mai ISO na ma’auni na kasa da kasa, wanda tawagar bincike karkashin jagorancin kwararrun Sinawa suka tsara, mai suna motar asibiti mai dakin kebance mara lafiya wato “Negative Pressure Ambulance Medical Cabin Technical Specifications”.

Wadannan motocin asibiti masu dakin kebance mara lafiya suna da kayan aikin jinya masu muhimmanci, galibi ana amfani da su don kebe mara lafiya cikin aminci yayin da ake jigilarsu, kuma suna taka muhimmiyar rawa wajen kula da cututtuka daban-daban na numfashi.

Wannan ma’auni na kasa da kasa ya gabatar da bukatun fasaha a karon farko wanda ya kamata a samar a cikin irin wadannan motocin asibiti masu dakin kebance mara lafiya, kuma yana tabbatar da cewa za a iya bayar da karin hidimomin jinya da kayayyakin aikin dake cikin motar a yayin da ake jigilar marasa lafiya.

Fitar da wannan ma’auni ya gabatar da kayyadaddun kayayyakin aiki da ake bukata a cikin wadannan motocin asibiti masu dakin kebance mara lafiya, wanda zai zama abin koyi ga kasashen duniya, kuma zai yi tasiri mai kyau a kan rigakafi da kula da cututtukan numfashi a duniya. Kwararru daga kasashen Sin, Faransa, Italiya da sauran kasashe suka yi hadin gwiwa wajen bincike da tsara wannan ma’auni. (Mai Fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: dakin kebance mara lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka

Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda ya tattauna ta wayar tarho da jami’ar harkokin waje ta tarayyar turai ya bayyana cewa, ci gaba da tattaunawa a tsakanin Iran da Amurka ba shi da wata ma’ana, kamata ya yi jami’an tarayyar turai din su yi Allawadai da wuce gona da irin HKI akan Iran.

Da safiyar yau Asabar ne dai jami’ar diplomasiyyar ta turai Kaja Kallas ta kira yi minsitan harkokin wajen jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci inda su ka tattauna halin da ake ciki a yammacin Asiya da ya hada da harin da HKI ta kawo wa Iran.

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana harin na HKI da cewa, wuce gona da iri ne da keta hurumin kasar Iran, kuma harin da ta kai wa cibiyoyin Nukiliya ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama da su ka hada da malaman jami’oi , da kuma mata da kananan yara.

Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su yi Allawadai da abinda HKI ta yi na take dokokin kasa da kasa.

Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Jamhuriyar musulunci ta Iran ya yi ishara da cewa, kudurin da majalisar alkalai ta hukumar makamashin Nukiliyar Iran ta fitar akan Iran wanda kuma kasashe uku na turai tare da Amurka su ka gabatar da shi, shi ne ya bude wa ‘yan Sahayoniya mashigar da su ka yi amfani da ita wajen wuce gona da iri akan Iran.

A nata gefen babbar jami’ar diplomasiyyar tarayyar turai ta bayyana rashin jin dadinta akan abinda yake faruwa a cikin yankin na yammacin Asiya na rikice-rikice, tare da bayyana cewa suna goyon bayan aiki da diplomasiyya domin tabbatar da zaman lafiya.

A wani labarin mai alaka da wannan kasar Oman ta sanar da cewa, ba za a yi taron da aka shirya yi a tsakanin Iran da Amruka ba.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ce ta fitar da sanarwar cewa; Tattaunawar da aka shirya cewa za a yi a tsakanin Amurka da Iran ba za a yi ta ba a gobe Lahadi.

Ministan harkokin wajen na Oman ya kara da cewa; Diplomasiyya ce kadai ya kamata ta zama hanyar cimma zaman lafiya mai dorewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu