An Gabatar Da Motar Asibiti Ta Farko Mai ISO Na Matsayin Kasa Da Kasa A Hukumance
Published: 10th, March 2025 GMT
A kwanan nan ne aka fitar da motar daukar mara lafiya ta farko mai ISO na ma’auni na kasa da kasa, wanda tawagar bincike karkashin jagorancin kwararrun Sinawa suka tsara, mai suna motar asibiti mai dakin kebance mara lafiya wato “Negative Pressure Ambulance Medical Cabin Technical Specifications”.
Wadannan motocin asibiti masu dakin kebance mara lafiya suna da kayan aikin jinya masu muhimmanci, galibi ana amfani da su don kebe mara lafiya cikin aminci yayin da ake jigilarsu, kuma suna taka muhimmiyar rawa wajen kula da cututtuka daban-daban na numfashi.
Fitar da wannan ma’auni ya gabatar da kayyadaddun kayayyakin aiki da ake bukata a cikin wadannan motocin asibiti masu dakin kebance mara lafiya, wanda zai zama abin koyi ga kasashen duniya, kuma zai yi tasiri mai kyau a kan rigakafi da kula da cututtukan numfashi a duniya. Kwararru daga kasashen Sin, Faransa, Italiya da sauran kasashe suka yi hadin gwiwa wajen bincike da tsara wannan ma’auni. (Mai Fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: dakin kebance mara lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota
Aƙalla ɗalibai takwas na Jami’ar Jos ne aka ruwaito sun mutu, yayin da wasu uku suka samu munanan raunuka, a wani mummunan hatsarin da ya rutsa da wata tirela da wata motar bas.
Hatsarin ya faru ne a hanyar Zariya, cikin ƙaramar hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.
NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a YobeLamarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na tsakar daren ranar Alhamis lokacin da ɗaliban ke dawowa daga wani biki.
Jami’in kula da wayar da kan jama’a na hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) Peter Yakubu Longsan ne ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa motar bas ɗin na ɗauke da ɗalibai 11 na Jami’ar.
A cewar Hukumar ta FRSC, shaidun gani da ido sun danganta hatsarin da tsananin gudu na direban motar yake yi na wuce gona da iri.
Da yake bayar da cikakken bayani kan lamarin, Longsan ya bayyana cewa, “A yau 11 ga Disamba, 2025, Hukumar FRSC reshen Jihar Filato ta samu kiran waya da misalin ƙarfe 02:30 na tsakar dare, inda aka ba da rahoton wani haɗarin mota da ya afku a kusa da hanyar Zariya wajen Unity Bank, a Jos.
“Hatsarin ya haɗa da motoci biyu, tirela da bas, mutum 11 ne a cikin motar kuma an ce ɗaliban jami’ar Jos ne. Da faruwar lamarin ne mutum bakwai ake zargin nan take sun mutu, domin daga ƙarshe likita ya tabbatar da cewa sun mutu, sai kuma wani da ya mutu a asibitin wanda ya kawo adadin waɗanda suka mutu zuwa takwas.
“A yanzu haka wasu uku suna karɓar magani a asibitin, dukkan waɗanda abin ya rutsa da su maza ne, kamar yadda wani ganau ya shaida cewar motar bas ɗin na cikin tsananin gudu, lamarin da ya kai ga rasa natsuwa daga bisani kuma lamarin ya faru. A halin yanzu dai ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike,” in ji shi.