Hukumar Alhazai Ta Kaduna Ta Nemi Goyon Bayan Sarkin Zazzau Don Nasarar Aikin Hajjin Bana
Published: 28th, February 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna (KSPWA) ta yaba da gudunmuwar da Gwamnatin Jihar Kaduna Malam Uba Sani ya ke badawa wajen samun nasarorin da aka samu kwanan nan.
An bayyana hakan ne a yayin wata ziyarar girmamawa da Shugaban Hukumar Jindadi Alhazai na Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar ya jagoranta tare da tawagar Kwamitin Musamman na Hajji da shugabannin ga Sarkin Zazzau, Malam Nuhu Bamalli, a fadarsa da ke Zariya.
Babban burin ziyarar shi ne neman ci gaba da samun goyon baya da addu’o’in Sarkin don samun nasarar ayyukan Hajji na shekarar 2025.
Malam Salihu ya nuna godiya sosai ga gudunmuwar da Sarkin ya ba da a baya kan shirye-shiryen Hajji, tare da jaddada muhimmancin cigaba da wannan hadin kai.
Ya ce, “Goyon bayan Gwamnatin Jihar Kaduna ga jin dadin alhazanmu abin alfahari ne. Tallafi daga dukkan fannoni, ciki har da na kudi ya taimaka mana sosai wajen cimma nasarorinmu. Wannan irin goyon bayan ya bambanta Hukumar ta Kaduna da takwarorinta.”
Malam Salihu ya kara da cewa hukumar ta riga ta yi rijistar alhazai 3,480 don lokacin Hajji mai zuwa kuma ta kaddamar da shirin wayar da kan alhazai.
Wannan shirin yana da nufin ilmantar da alhazai game da yadda ake gudanar da ibadar Hajji, dokoki, da koyarwar addinin Musulunci.
A nasa jawabin, Sarkin Zazzau, Malam Ahmad Nuhu Bamalli, ya yabawa Kwamitin Musamman na Hajji kan gyare-gyaren da suka kawo a hukumar.
Ya jaddada cewa wadannan gyare-gyaren suna da matukar muhimmanci wajen tabbatar da cewa alhazan sun amfana da kudaden da suka kashe wajen tafiya Saudiyya.
Sarkin ya yi kira da a ilmantar da alhazai kan haramcin daukar kaya haram zuwa Kasar Saudiyya don kauce wa samun matsala da hukumomin Saudiyya.
Ya kuma roki Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Saudiyya da su ci gaba da yin aiki tare da Hukumar Hajji ta Kasa domin tabbatar da cewa alhazan Najeriya sun samu kima da mutunci a tsawon zamansu.
Rel/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai Ta Kaduna Ta Nemi Goyon Bayan Sarkin Nasarar
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
Dabbobi sama da miliyan guda ne ake sa ran za a yi wa rigakafi a fadin karamar hukumar Babura da ke jihar Jigawa.
Shugaban karamar hukumar Babura, Alhaji Hamisu Muhammad Garu, ne ya bayyana hakan yayin kaddamar da aikin rigakafin dabbobi na bana.
A cewarsa, fiye da tumaki da awaki miliyan daya da shanu dubu ashirin ake sa ran za a yi wa rigakafi a fadin karamar hukumar.
Ya jaddada cewa karamar hukumar na da cikakken shiri da kudurin tallafawa sauyin noma na Gwamna Umar Namadi, domin inganta rayuwa da tattalin arzikin al’ummar jihar.
Shugaban ya jaddada muhimmancin masu kiwon dabbobi su bada hadin kai yayin aikin rigakafin domin tabbatar da lafiyar dabbobinsu.
Alhaji Hamisu Garu ya kuma nuna jin dadinsa game da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya a yankin, yana mai kira gare su da su ci gaba da gudanar da rayuwa cikin fahimta da hadin kai.
Haka zalika, yayin taron, Shugaban Sashen Noma da Albarkatun Kasa, Malam Lawan Sabo Kaugama, ya bayyana cewa an ware cibiyoyi guda goma sha biyu domin gudanar da aikin rigakafin wanda ake sa ran zai dauki kwanaki hudu.
Ya yaba da kokarin gwamnatin jiha da ta karamar hukuma wajen samar da allurar rrigakafn da kuma duk wasu kayan aiki da ake bukata.
Usman Muhammad Zaria