Hukumar Alhazai Ta Kaduna Ta Nemi Goyon Bayan Sarkin Zazzau Don Nasarar Aikin Hajjin Bana
Published: 28th, February 2025 GMT
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna (KSPWA) ta yaba da gudunmuwar da Gwamnatin Jihar Kaduna Malam Uba Sani ya ke badawa wajen samun nasarorin da aka samu kwanan nan.
An bayyana hakan ne a yayin wata ziyarar girmamawa da Shugaban Hukumar Jindadi Alhazai na Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar ya jagoranta tare da tawagar Kwamitin Musamman na Hajji da shugabannin ga Sarkin Zazzau, Malam Nuhu Bamalli, a fadarsa da ke Zariya.
Babban burin ziyarar shi ne neman ci gaba da samun goyon baya da addu’o’in Sarkin don samun nasarar ayyukan Hajji na shekarar 2025.
Malam Salihu ya nuna godiya sosai ga gudunmuwar da Sarkin ya ba da a baya kan shirye-shiryen Hajji, tare da jaddada muhimmancin cigaba da wannan hadin kai.
Ya ce, “Goyon bayan Gwamnatin Jihar Kaduna ga jin dadin alhazanmu abin alfahari ne. Tallafi daga dukkan fannoni, ciki har da na kudi ya taimaka mana sosai wajen cimma nasarorinmu. Wannan irin goyon bayan ya bambanta Hukumar ta Kaduna da takwarorinta.”
Malam Salihu ya kara da cewa hukumar ta riga ta yi rijistar alhazai 3,480 don lokacin Hajji mai zuwa kuma ta kaddamar da shirin wayar da kan alhazai.
Wannan shirin yana da nufin ilmantar da alhazai game da yadda ake gudanar da ibadar Hajji, dokoki, da koyarwar addinin Musulunci.
A nasa jawabin, Sarkin Zazzau, Malam Ahmad Nuhu Bamalli, ya yabawa Kwamitin Musamman na Hajji kan gyare-gyaren da suka kawo a hukumar.
Ya jaddada cewa wadannan gyare-gyaren suna da matukar muhimmanci wajen tabbatar da cewa alhazan sun amfana da kudaden da suka kashe wajen tafiya Saudiyya.
Sarkin ya yi kira da a ilmantar da alhazai kan haramcin daukar kaya haram zuwa Kasar Saudiyya don kauce wa samun matsala da hukumomin Saudiyya.
Ya kuma roki Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Saudiyya da su ci gaba da yin aiki tare da Hukumar Hajji ta Kasa domin tabbatar da cewa alhazan Najeriya sun samu kima da mutunci a tsawon zamansu.
Rel/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai Ta Kaduna Ta Nemi Goyon Bayan Sarkin Nasarar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
Ma’aikatar Gona da tsaron abinci ta tarayya ta sanar da gudanar da addu’a da azumi na kwanaki uku domin neman taimakon Allah wajen kare ƙasar nan da kuma tabbatar da wadatar abinci. Wannan na ƙunshe ne a wata takarda da aka fitar a ranar 11 ga Yuni, 2025, wadda Daraktar Gudanarwa, Mrs. Adedayo Modupe O., ta sanya wa hannu.
A cewar sanarwar, dukkanin daraktoci, da mataimakan daraktoci, da shugabannin sassan sarrafa kayayyakin amfanin gona da sauran ma’aikatan ma’aikatar za su halarta. An sanya wa wannan shiri suna “Neman Taimakon Ubangiji Don Kariya da Cigaban Kasa.”
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA Gwamnatin Gombe Ta Yi Albishir Ɗin Gina Babban Zangon Noma Da Kiwo Ɗauke Da Kasuwar Duniya A JiharModupe ta bayyana cewa manufar wannan addu’a ita ce neman jagorancin Allah da tallafinsa ga ƙoƙarin gwamnati wajen samar da ingantaccen tsarin abinci mai ɗorewar a fadin ƙasa. Za a gudanar da zaman addu’ar ne a shalƙwatar ma’aikatar da ke Abuja a ranakun Litinin: 16, 23 da 30 ga Yuni, 2025.
Sanarwar ta buƙaci dukkan ma’aikata su kasance cikin azumi domin samun tsarkakewa da shiri na musamman wajen roƙon Allah game da matsalolin da ke addabar fannin noma da tsaron abinci a Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp