Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa
Published: 28th, February 2025 GMT
Cibiyar Bunƙasa Ayyukan Bincike za ta gudanar da gangami domin nazarin dokokin da suka shafi zamantakewar Musulmi a jihohin da ta ke aiki, domin inganta haƙƙoƙin mata da ƙananan yara.
Shugaban tawagar cibiyar, Dokts Taofik Abubakar daga Jami’ar Bayero Kano ne, ya bayyana hakan yayin wata ziyarar girmamawa da suka kai wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, a fadarsa da ke Zariya.
Dokta Taofik, ya ce sun je fadar ne, domin neman albarka da shawarwari kan hanyoyin magance cin zarafin mata.
Ya kuma bayyana cewa cibiyar ta ɗauki nauyin malamai da limamai zuwa Jami’ar Al-Azhar da ke Masar don ƙaro ilimi kan matsayin Musulunci game da cin zarafin mata.
A cewarsa, cin zarafin mata al’ada ce da aka gada daga tsohuwar ɗabi’a, ba addinin Musulunci ba.
Ya ƙaryata fahimtar da wasu ke da ita cewa Musulunci yana goyon bayan miji ya doki matarsa, inda ya jaddada cewa Annabi Muhammad (SAW), ya haramta hakan.
Cibiyar za ta gudanar da gangamin tattaunawa da shugabannin jihohin Kano da Kaduna domin nazarin dokokin da suka shafi zamantakewar Musulmi, tare da ƙoƙarin tabbatar da su matsayin doka.
A nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya buƙaci a sake nazarin dokar zamantakewar Musulmi da aka yi watsi da ita a Kano, domin inganta haƙƙoƙin mata a Arewacin Najeriya.
Ya bayyana cewa haƙƙoƙin mata ba su da ƙarfi a tsarin dokokin shari’a na yankin, wanda ke haifar da cikas ga rayuwarsu.
Ya ce idan aka tabbatar da dokar, zai taimaka wajen kare haƙƙin mata da yara a Arewa.
Sarkin ya kuma buƙaci da a gaggauta tabbatar da dokar a jihohin da ake gudanar da aikin, domin ta zama doka da za a bi a duk faɗin Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Cibiya Sarkin Zazzau yara Zariya tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
Gwamnatin Jihar Kano ta musanta zargin da wasu ke yi cewa ta karɓo sabon bashi na dala miliyan 6.6 daga watan Yuni zuwa Disamba 2023, tana mai cewa wannan zargi ƙarya ne marar tushe da aka ƙirƙira domin ɓata mata suna. Wannan na zuwa ne bayan wata ƙungiyar siyasa mai suna APC Patriotic Volunteers ta yi zargin cewa gwamnatin NNPP mai ci a jihar ta karɓo bashi daga ƙasashen waje ba tare da bayyana hakan ba.
Darakta Janar na Ofishin Gudanar da Basussuka a jihar, Dr. Hamisu Sadi Ali, ya bayyana cewa tun daga lokacin da gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta hau mulki, ba ta karɓi wani sabon bashi ko na gida ko na waje ba, balle a ɓoye shi daga idon jama’a. Ya ce duk wani bashi da gwamnatin jihar ke aiki da shi a halin yanzu an gada ne daga gwamnatin da ta gabata.
Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa Sarki Sanusi II Ya Yi Hawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda Na Haramta Hawan Sallah A KanoDr. Ali ya kuma ƙalubalanci tsohon Sakataren Gwamnatin Jiha, Alhaji Usman Alhaji, wanda ya jagoranci ƙungiyar da ta yi zargin, yana mai cewa duk wanda ke da hujjar wannan zargi ya fito da takardun da ke tabbatar da hakan – ciki har da sunan mai bayar da bashin, kwafen yarjejeniyar, dalilin karɓa, da tsarin biyan bashin.
A cewarsa, akwai doka mai ƙarfi da ke kula da basussuka a jihar, wadda gwamnatin APC ta gabata ta kafa a 2021. Wannan doka ta bai wa ofishinsa ikon karɓar bashi cikin tsarin doka da cikakken sahihanci, kuma ba wani bashi da aka karɓa tun bayan 2023. Ya ce gwamnati na gudanar da harkokinta cikin gaskiya da rikon amana, kuma ba za ta lamunci ƙarya da siyasar ɓatanci ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp