Aminiya:
2025-05-01@04:29:53 GMT

Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa

Published: 28th, February 2025 GMT

Cibiyar Bunƙasa Ayyukan Bincike za ta gudanar da gangami domin nazarin dokokin da suka shafi zamantakewar Musulmi a jihohin da ta ke aiki, domin inganta haƙƙoƙin mata da ƙananan yara.

Shugaban tawagar cibiyar, Dokts Taofik Abubakar daga Jami’ar Bayero Kano ne, ya bayyana hakan yayin wata ziyarar girmamawa da suka kai wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, a fadarsa da ke Zariya.

Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki

Dokta Taofik, ya ce sun je fadar ne, domin neman albarka da shawarwari kan hanyoyin magance cin zarafin mata.

Ya kuma bayyana cewa cibiyar ta ɗauki nauyin malamai da limamai zuwa Jami’ar Al-Azhar da ke Masar don ƙaro ilimi kan matsayin Musulunci game da cin zarafin mata.

A cewarsa, cin zarafin mata al’ada ce da aka gada daga tsohuwar ɗabi’a, ba addinin Musulunci ba.

Ya ƙaryata fahimtar da wasu ke da ita cewa Musulunci yana goyon bayan miji ya doki matarsa, inda ya jaddada cewa Annabi Muhammad (SAW), ya haramta hakan.

Cibiyar za ta gudanar da gangamin tattaunawa da shugabannin jihohin Kano da Kaduna domin nazarin dokokin da suka shafi zamantakewar Musulmi, tare da ƙoƙarin tabbatar da su matsayin doka.

A nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya buƙaci a sake nazarin dokar zamantakewar Musulmi da aka yi watsi da ita a Kano, domin inganta haƙƙoƙin mata a Arewacin Najeriya.

Ya bayyana cewa haƙƙoƙin mata ba su da ƙarfi a tsarin dokokin shari’a na yankin, wanda ke haifar da cikas ga rayuwarsu.

Ya ce idan aka tabbatar da dokar, zai taimaka wajen kare haƙƙin mata da yara a Arewa.

Sarkin ya kuma buƙaci da a gaggauta tabbatar da dokar a jihohin da ake gudanar da aikin, domin ta zama doka da za a bi a duk faɗin Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Cibiya Sarkin Zazzau yara Zariya tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ya bayyana kalaman gwamnatin ‘yan sahayoniyya a matsayin wani rudu da ba shi da amfani da har zai yi tasiri a zaman tattaunawan Iran da Amurka Wanda ba na kai tsaye ba, yana mai cewa duk wani hari ko da karami ne za a kai kan Iran zai zama tamkar tartsatsin wuta da zai iya janyo tashin gobara da zai iya kona yankin gaba daya.

A jawabin da ya gabatar yayin taron kolin majalisar shawarar Musulunci ta Iran a yau Talata, Muhammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa: Firai ministan gwamnatin yahudawan sahayoniyya mai laifi ne mai zubar da jinin fararen hula, saboda neman hana mutuwarsa a fagen siyasa, kuma yanzu yana yin barazana ga al’ummar Iran mai girma. Qalibaf ya yi nuni da cewa, wannan mutum mai rauni yana son canza haryar tafiyarsa a kullum rana saboda tsoron kada a kama shi sakamakon kasancewarsa mai laifi da yafi zama abin ki a tarihin wannan zamani.

Qalibaf ya kara da cewa; Bayan shafe shekaru da dama Netanyahu yana yaudarar kafafen yada labarai, a halin yanzu gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta fito fili kuma ta bayyana hakikanin fuskar wannan azzalumi ga duniya, musamman ga matasan Amurka da Turai. Qalibaf ya kara da cewa babu wani abin da wannan gwamnatin ta cimma sai kai hare-haren bama-bamai kan makarantu da asibitoci, kuma ba ta cimma burin da ta ayyana a farkon yakin ba, kuma halin da ake ciki yana da matukar rashin tabbas.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara