Leadership News Hausa:
2025-08-01@10:50:06 GMT

NAHCON Ta Naɗa Sabon Sakatare

Published: 28th, February 2025 GMT

NAHCON Ta Naɗa Sabon Sakatare

Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta sanar da naɗin Dakta Mustapha Muhammad Ali, a matsayin sabon Sakataren Hukumar.

Sanarwar naɗin na ƙunshe ne a cikin wata takarda da shugaban sashin hulɗa da Jama’a na hukumar, Muhammad Ahmad Musa, ya fitar bayan amincewar kwamitin gudanarwa na NAHCON a taron da aka gudanar na ranar 26 ga Fabrairun 2025, bisa tanadin sashi na 8 na dokar da ta kafa NAHCON ta 2006.

NAHCON Ta Tsawaita Wa’adin Biyan Kuɗin Kujerar Aikin Hajjin 2025 zuwa 10 ga Fabrairu Hajjin 2025: Kamfanin Saudiyya Ya Amince Da Kwangilar Aiki Da NAHCON Bayan Sabunta Yarjejeniya 

Dakta Mustapha Muhammad Ali, wanda ƙwararre ne wajen tabbatar da gudanarwa da kuma aiwatar da manufofin inganta aikin Hajji a Nijeriya, zai yi aiki a matsayin Sakatare na tsawon shekaru huɗu a matakin farko.

Kazalika gogaggen ma’aikaci ne kuma tsohon babban Sakataren hukumar Jin daɗin Alhazai ta Jihar Borno, kana yana da ƙwarewa mai yawa da zai kawo wa hukumar ci gaba a ayyukanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

 

Dandali na NINAuth, wanda NIMC ya tsara kuma ya aiwatar, yana bayar da damar tantance bayanan ‘yan kasa ta hanya mafi dacewa da aminci don tabbatar da asalinsu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura