Aminiya:
2025-08-13@14:39:16 GMT

Mun san inda Bello Turji yake —Sojoji

Published: 24th, February 2025 GMT

Babban Jami’in Ayyuka na Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya, Manjo-Janar Emeka Onumajuru, ya bayyana cewa saura kiris su gama da jagoran ’yan ta’adda, Bello Turji.

Manjo-Janar Emeka Onumajuru ya bayyana cewa sojojin suna kan bibiyar motsin Bello Turji, kuma sun gano inda yake, amma bai yi ƙarin bayani ba.

“Babu wani kwan-gaba-kwan-baya a wurin sojoji kan maganar Bello Turji, mun gano inda maɓoyarsa take,” in ji Janar Emeka.

Ya ci gaba da cewa a halin yanzu sojoji sun riga sun rutsa Turji a maɓoyarsa, babu inda zai iya motsawa ya je, saboda tsoro

Ya bayyana haka ne a safiyar Litinin yana mai cewa kwanakon Turji sun kusa karewa.

Janar din ya bayyana haka ne a yayin hirar da gidan talabijin na Channels ya yi da shi a ranar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’ani

Wani mutum ya ba da kyautar motarsa da ita kadai gare shi ga wani mai jan baki (alaramma) saboda ƙwarewarsa a haddar Al-kur’ani.

Malam Yusuf Ɗan-Birni, ya kyautar da motar ce a taron wa’azin wata-wata da Ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa Iƙamatis Sunna (JIBWIS) ta shirya a garin Kubwa da ke yankin Babban Birnin Tarayya.

Malam Yusuf Ɗan-Birni wanda ke sana’ar gyaran waya, ya bai wa jama’a mamaki a yayin da ake tsaka da karatun da misalin ƙarfe 10 nan dare inda ya miƙa makullan motarsa ga mai gabatar da wa’azin, Sheikh Mahmud Assalafi, ya sanar da shi cewa ya kyautar da ita ga majabaƙinsa, Alaramma Usman Nasidi Gusau.

Wani ganau mai suna Malam Nuhu Abu-Huzaifa ya shaida wa Aminiya cewa, wanda ya kyautar da motar na zaune a kusa da shi, sai ya lura yana zubar da ƙwalla a lokacin da alaramman ke karanta Alƙur’ani Mai Tsarki.

Malam Nuhu ya bayyana cewa, “Malami mai fassara Sheikh Mahmud Assalafi ya yi ta yawatawa da alaramman a cikin ayoyi da surorin Wlqur’ani ta hanyan ƙidayo masa surorin da kuma ayoyin, a inda alaramman ke gano su nan take a cikin sauki.”

Ya ce bayan kammala wa’azin da misalin ƙarfe 11 na dare ya ga wanda ya yi kyautar motar ya tsayar da ɗan acaɓa zai hau da nufin komawa gida.

Ya yi addu’ar Allah Ya daɗaɗa wa Yusuf Ɗan-Birni da iyalansa kamar yadda ya daɗaɗa wa Alaramman, Ya kuma maye masa gurbin motar da ya kyautar da wadda ta fita ta.

A zantawarsa da Aminiya a kan lamarin, Babban Limamin Masallacin Badar da ke Garin na Kubwa inda taron ya gudana, sheikh Abdulmumini Ahmad Khalid, ya nuna farin ciki a kan lamarin tare da bayyana kyautar a matsayin abin da ba kasafai yake faruwa ba.

Ya ce, ba a fi wata guda ba, Dan-Birni ya zo da motar da ya saya ƙirar Fijo 406, cewa ya saye ta domin zirga-zirga da na’urorin daukar karatu a bidiyo da sauran ayyukan masallacin, da yake watsawa ta dandalin sada zumunta.

Ya yi addu’ar Allah Ya saka masa da mafi alheri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello
  • Iran: Janar Hatami ya karbi bakuncin babban hafsan hafsoshin sojin Afirka ta kudu
  • Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.
  • Yadda ɗan shekara 70 ya rasu a gobarar tankokin gas a Zariya
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
  • Mahukuntan Iraki Sun Bayyana Cewa: Akwai Yiwuwar Masu Ziyarar Arba’een Na Imam Husaini {a.s} Zasu Zarce Miliyan 4
  • Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’ani
  • Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA
  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali