HausaTv:
2025-06-15@05:58:44 GMT

Pezeshkian: Hizbollah tana nan a raye a kan tafarkin gwagwarmaya

Published: 24th, February 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa matukar aka samu mamaya to za a samu manyan mutane irin shahid Sayyeed Hasan Nasrallah da za su tsaya tsayin daka kan yaki da hakan, kuma ba za su bari ‘yan mamaya su cimma manufarsu ba.

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa, Hizbullah tana nan a raye kuma tana ci gaba da bin tafarkinta mai daraja fiye da kowane lokaci a baya.

A yayin zaman majalisar ministocin kasar Iran, Pezeshkian ya bayyana cewa, matukar dai abin ake yi na zalunci da danniya a kan masu rauni zai ci gaba, to kuwa tabbas ba za a rasa mutane irin Nasrallah ba, masu tsayin daka da jajircewa wajen tunkarar zalunci da mamaya.

Shugaban kasar Iran ya jinjinawa shahidan gwagwarmaya da suka hada da Sayyed Hassan Nasrallah, tare da tunawa da sadaukarwa ta dukkanin mujahidan da suka yi shahada suka yi a yayin karawa da haramtacciyar kasar Isra’ila.

Bazeshkian ya yi nuni da cewa: “Masu da’awar cewa gwagwarmaya za ta ruguje tare da shahadar Sayyid Nasrallah, a maimakon haka, Hizbullah ta ci gaba da kara jajircewa ne a kan matsayinta na yaki da zalunci da mamaya ta sahyuniyawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka

Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda ya tattauna ta wayar tarho da jami’ar harkokin waje ta tarayyar turai ya bayyana cewa, ci gaba da tattaunawa a tsakanin Iran da Amurka ba shi da wata ma’ana, kamata ya yi jami’an tarayyar turai din su yi Allawadai da wuce gona da irin HKI akan Iran.

Da safiyar yau Asabar ne dai jami’ar diplomasiyyar ta turai Kaja Kallas ta kira yi minsitan harkokin wajen jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci inda su ka tattauna halin da ake ciki a yammacin Asiya da ya hada da harin da HKI ta kawo wa Iran.

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana harin na HKI da cewa, wuce gona da iri ne da keta hurumin kasar Iran, kuma harin da ta kai wa cibiyoyin Nukiliya ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama da su ka hada da malaman jami’oi , da kuma mata da kananan yara.

Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su yi Allawadai da abinda HKI ta yi na take dokokin kasa da kasa.

Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Jamhuriyar musulunci ta Iran ya yi ishara da cewa, kudurin da majalisar alkalai ta hukumar makamashin Nukiliyar Iran ta fitar akan Iran wanda kuma kasashe uku na turai tare da Amurka su ka gabatar da shi, shi ne ya bude wa ‘yan Sahayoniya mashigar da su ka yi amfani da ita wajen wuce gona da iri akan Iran.

A nata gefen babbar jami’ar diplomasiyyar tarayyar turai ta bayyana rashin jin dadinta akan abinda yake faruwa a cikin yankin na yammacin Asiya na rikice-rikice, tare da bayyana cewa suna goyon bayan aiki da diplomasiyya domin tabbatar da zaman lafiya.

A wani labarin mai alaka da wannan kasar Oman ta sanar da cewa, ba za a yi taron da aka shirya yi a tsakanin Iran da Amruka ba.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ce ta fitar da sanarwar cewa; Tattaunawar da aka shirya cewa za a yi a tsakanin Amurka da Iran ba za a yi ta ba a gobe Lahadi.

Ministan harkokin wajen na Oman ya kara da cewa; Diplomasiyya ce kadai ya kamata ta zama hanyar cimma zaman lafiya mai dorewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar
  • Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike