Aminiya:
2025-07-31@18:51:09 GMT

Abin da ya sa na yi wa Buhari juyin mulki —Babangida

Published: 24th, February 2025 GMT

Tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (murabus) ya bayyana dalilin da ya hambarar da gwamnatin Janar Muhammadu Buhari a 1985.

Janar Babangida ya bayyana dalilin da gwamnatinsa ta karya darajar Naira da sauran sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ta yi bayan kifar da Buhari.

Babangida, wanda shi ne babban hafsan sojin kasa a lokacin Buhari, ya taka rawar gani a juyin mulkin da aka yi wa Shugaba Shehu Usman Shagari a 1983 da kuma na 1985 da ya kawo shi kan karagar mulki.

Ya ba da cikakken bayani game da abubuwan da suka faru a cikin littafin tarihin rayuwarsa da ya ƙaddamar a makon jiya.

Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri

Littafin na Babangida ya haifar da cece-kuce, game da muhimman batutuwan da suka dabaibaye mulkinsa na shekaru takwas, musamman soke zaben shugaban kasa na ranar 12 ga watan Yuni; kashe babban dan jarida, Dele Giwa; da kuma kashe Manjo Janar Mamman Vatsa bisa zargin yunkurin juyin mulki.

 “Juyin mulkin 1985 ya zama dole.”

A babi na shida, Babangida ya ba da hujjar juyin mulkin da aka yi wa Janar Buhari a 1985. Ya bayyana cewa juyin mulkin martani ga korafe-korafen ’yan Najeriya da kuma tabarbarewar al’amurana kasar.

Ya ce, “A farkon shekarar 1985, ’yan Najeriya sun fara fargaba game da makomar kasarmu. Al’amarin ya kasance mai hadari kuma yana cike da munanan alamun a fili da hatsarin da ke yanzu.

“A bayyane yake ga shugabancin sojojin cewa aikin da muka yi da nufin ceto ƙasarmu a shekarar 1983 ya watse,” kamar yadda Janar Babangida ya rubuta.

Ya ce rashin daukar mataki zai kawo rarrabuwar kawuna a tsakanin sojoji, wanda a ganinsa hakan zai haifar da mummunar illa ga kasar.

“Idan sojojin suka yi samu rabuwar kai, al’ummar za su bi sahu, kuma abin da zai biyo baya zai zama mai ban tsoro ne da ba za a iya tunani ba,” in ji shi.

A cewarsa, a shekarar 1983 sojoji sun hambarar da Shugaba Shagari ne cikin haɗin kai, amma sai aka fara samun rarrabuwar kawuna tsakaninsu.

“Sojoji, a matsayinsu na waɗanda aka sani da hadin kai, sai ga shi an fara samun guna-guni; down haka ya zama dole a yi wani abu don kada mu rasa kasar.

“Babban abin da na ji tsoro shi ne, rarrabuwar kawuna da ra’ayi a tsakanin sojoji na iya haifar da bangaranci a tsakaninsu. Idan kuma aka bari a ci gaba da samun gindin zama, to akwai hatsarin gaske.”

Ya zargi Buhari da mataimakinsa Birgediya Janar Tunde Idiagbon da mayar da mayar da sojoji saniyar ware, tare da daukar tsauraran matakan kama-karya wajen tafiyar da mulki.

“Sun dauki kansu kamar wasu waliyyai, inda suka kawo wa sojoji bakin jini a wurin al’ummar kasa. Suna take hakkin al’umma tare da cin zarafi babu kakkautawa,” in ji Babangida.

A cewarsa gwmanatin sojin Buhari ta yi mulki ne ta hanyar tsoratarwa maimakon sanya ’yan kyakkyawan fata a zukatan al’umma.

“Kamata ya yi mu Inganta rayuwarsu mu sa musu kyakkyawan fata cewa rayuwarsu za ta inganta. Amma maimakon haka sai aka yi ta kafa musu dokokin kama-karya.

“Sai aka wayi gari gwamnatin da aka kafa da niyyar cimma muradun bai-ɗaya na sojoji, ta koma ta wasu ’yan tsirarun mutane masu taurin kai,” in ji Babangida.

Taɓarɓarewar tattalin arziki

Ya bayyana cewa tsarin musayar kaya na gargajiya da Buhari ya koma amfani da shi ya kara kassara tattalin arzikin Najeriya.

Ya ƙara da cewa lalacewar tattalin arziki da guna-gunin ’yan kasa kan matsin rayuwa na daga cikin abin da suka sa su hambarar da Buhari.

Ya ce, “Kamar yawancin juyin mulkin soja, mun yi ne sakamakon yawan korafe-korafen jama’a. Talakawa sun shiga matsanancin matsin rayuwa, ga shi yanayin tattalin arziki sai kara  ta’azzara suke yi a kulla-yaumin.

“Kayayyakin masarufi da sauran bukatun yau da kullum sai karanci suke kara yi.

“Sannan ku a komawa amfani da  tsohuwar hanyar yin ciniki ta hanyar musayar kaya a kasuwancin kasa da kasa yana nufin cewa ba a kama hanyar kawo karshen matsalolin tattalin arziki a tsakanin al’umma ba.

Dokokin kama-karya, sun tauye ’yancin walwalar jama’a, ga kuma hukunci mai tsauri, in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari tattalin arziki Babangida ya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.

Shugaban marasa rinjaye na Majalisar Wakilai Ali Isah, ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na Majalisar bayan wata ganawa da mai kula da jihar Ribas Sole a Abuja.

 

Ali Isah, ya bayyana cewa mai kula da jihar ta Ribas ya kasance a gidan a wani bangare na ziyarar da ya saba yi domin yiwa kwamitin riko da ke sa ido kan al’amuran gwamnati.

 

Shugaban marasa rinjaye wanda ya jagoranci taron a madadin shugaban kwamitin wanda ya zama shugaban masu rinjaye na majalisar Farfesa Julius Ihonvere, ya bayyana gamsuwa da kokarin da mai gudanarwa shi kadai yake yi na wanzar da zaman lafiya a jihar.

 

Ya ce mai kula da jihar ya tuntubi manyan masu ruwa da tsaki kan rikicin shugabancin jihar Ribas, shugabannin cibiyoyin addini da na gargajiya, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki don ganin an warware matsalar cikin ruwan sanyi domin ci gaban jihar.

 

Sai dai jami’in da ya gabata, ya umurci mai kula da shi kadai da ya tabbatar da cewa rikicin shugabancin jihar Ribas bai shafi biyan albashin ma’aikatan gwamnati da wadanda suka yi ritaya duk wata da fansho ba kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da majalisar dokokin kasar ke yin duk mai yiwuwa don tabbatar da mulkin dimokuradiyya a kasar nan.

 

Ali Isah, ya kuma tabbatar da cewa kwamitin wucin gadi zai ci gaba da tuntubar mai gudanarwa da bangaren zartarwa don hana tsawaita dakatarwar daga wa’adin watanni shida domin samun ci gaba.

 

COV: TSIBIRI

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa