Aminiya:
2025-05-01@06:33:40 GMT

Abin da ya sa na yi wa Buhari juyin mulki —Babangida

Published: 24th, February 2025 GMT

Tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (murabus) ya bayyana dalilin da ya hambarar da gwamnatin Janar Muhammadu Buhari a 1985.

Janar Babangida ya bayyana dalilin da gwamnatinsa ta karya darajar Naira da sauran sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ta yi bayan kifar da Buhari.

Babangida, wanda shi ne babban hafsan sojin kasa a lokacin Buhari, ya taka rawar gani a juyin mulkin da aka yi wa Shugaba Shehu Usman Shagari a 1983 da kuma na 1985 da ya kawo shi kan karagar mulki.

Ya ba da cikakken bayani game da abubuwan da suka faru a cikin littafin tarihin rayuwarsa da ya ƙaddamar a makon jiya.

Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri

Littafin na Babangida ya haifar da cece-kuce, game da muhimman batutuwan da suka dabaibaye mulkinsa na shekaru takwas, musamman soke zaben shugaban kasa na ranar 12 ga watan Yuni; kashe babban dan jarida, Dele Giwa; da kuma kashe Manjo Janar Mamman Vatsa bisa zargin yunkurin juyin mulki.

 “Juyin mulkin 1985 ya zama dole.”

A babi na shida, Babangida ya ba da hujjar juyin mulkin da aka yi wa Janar Buhari a 1985. Ya bayyana cewa juyin mulkin martani ga korafe-korafen ’yan Najeriya da kuma tabarbarewar al’amurana kasar.

Ya ce, “A farkon shekarar 1985, ’yan Najeriya sun fara fargaba game da makomar kasarmu. Al’amarin ya kasance mai hadari kuma yana cike da munanan alamun a fili da hatsarin da ke yanzu.

“A bayyane yake ga shugabancin sojojin cewa aikin da muka yi da nufin ceto ƙasarmu a shekarar 1983 ya watse,” kamar yadda Janar Babangida ya rubuta.

Ya ce rashin daukar mataki zai kawo rarrabuwar kawuna a tsakanin sojoji, wanda a ganinsa hakan zai haifar da mummunar illa ga kasar.

“Idan sojojin suka yi samu rabuwar kai, al’ummar za su bi sahu, kuma abin da zai biyo baya zai zama mai ban tsoro ne da ba za a iya tunani ba,” in ji shi.

A cewarsa, a shekarar 1983 sojoji sun hambarar da Shugaba Shagari ne cikin haɗin kai, amma sai aka fara samun rarrabuwar kawuna tsakaninsu.

“Sojoji, a matsayinsu na waɗanda aka sani da hadin kai, sai ga shi an fara samun guna-guni; down haka ya zama dole a yi wani abu don kada mu rasa kasar.

“Babban abin da na ji tsoro shi ne, rarrabuwar kawuna da ra’ayi a tsakanin sojoji na iya haifar da bangaranci a tsakaninsu. Idan kuma aka bari a ci gaba da samun gindin zama, to akwai hatsarin gaske.”

Ya zargi Buhari da mataimakinsa Birgediya Janar Tunde Idiagbon da mayar da mayar da sojoji saniyar ware, tare da daukar tsauraran matakan kama-karya wajen tafiyar da mulki.

“Sun dauki kansu kamar wasu waliyyai, inda suka kawo wa sojoji bakin jini a wurin al’ummar kasa. Suna take hakkin al’umma tare da cin zarafi babu kakkautawa,” in ji Babangida.

A cewarsa gwmanatin sojin Buhari ta yi mulki ne ta hanyar tsoratarwa maimakon sanya ’yan kyakkyawan fata a zukatan al’umma.

“Kamata ya yi mu Inganta rayuwarsu mu sa musu kyakkyawan fata cewa rayuwarsu za ta inganta. Amma maimakon haka sai aka yi ta kafa musu dokokin kama-karya.

“Sai aka wayi gari gwamnatin da aka kafa da niyyar cimma muradun bai-ɗaya na sojoji, ta koma ta wasu ’yan tsirarun mutane masu taurin kai,” in ji Babangida.

Taɓarɓarewar tattalin arziki

Ya bayyana cewa tsarin musayar kaya na gargajiya da Buhari ya koma amfani da shi ya kara kassara tattalin arzikin Najeriya.

Ya ƙara da cewa lalacewar tattalin arziki da guna-gunin ’yan kasa kan matsin rayuwa na daga cikin abin da suka sa su hambarar da Buhari.

Ya ce, “Kamar yawancin juyin mulkin soja, mun yi ne sakamakon yawan korafe-korafen jama’a. Talakawa sun shiga matsanancin matsin rayuwa, ga shi yanayin tattalin arziki sai kara  ta’azzara suke yi a kulla-yaumin.

“Kayayyakin masarufi da sauran bukatun yau da kullum sai karanci suke kara yi.

“Sannan ku a komawa amfani da  tsohuwar hanyar yin ciniki ta hanyar musayar kaya a kasuwancin kasa da kasa yana nufin cewa ba a kama hanyar kawo karshen matsalolin tattalin arziki a tsakanin al’umma ba.

Dokokin kama-karya, sun tauye ’yancin walwalar jama’a, ga kuma hukunci mai tsauri, in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari tattalin arziki Babangida ya

এছাড়াও পড়ুন:

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

Ba wannan ne karo na farko da shugaba Trump ya nuna girman kai da rashin sani game da Afirka ba. A watan da ya gabata, lokacin da yake bayani game da dalilin da ya sa gwamnatinsa ke rage gudummawar jin kai da take bayarwa a duniya, ya ce a baya, Amurka ta samar wa kasar Lesotho gudummawar dala miliyan 8, amma “ba wanda ya taba jin sunan wannan kasa”. Amma ita wannan kasar da ko sunanta shugaba Trump bai taba ji ba, ya sanya ta cikin jerin kasashen da ya sanar da zai kakaba musu haraji, har ma ya sanya mata haraji na kaso 50%. Idan ba mu manta ba kuma, a wa’adin shugabancinsa na farko, shugaba Trump ya taba bayyana kasashen Afirka a matsayin “shithole” a lokacin da ya tabo maganar bakin haure.

 

Sai dai ban da girman kai da rashin sani, kalaman shugaba Trump ya kuma bayyana matsayin da gwamnatin kasar Amurka ta dade tana dauka a game da kasashen Afirka, wato a maimakon abokan hadin gwiwa na zaman daidaito da martaba juna, tana kallonsu a matsayin abin da take iya amfani da su wajen takara da sauran manyan kasashe, kuma muna iya ganin haka ne daga manufofin da mahukuntan kasar suka dauka cikin ‘yan shekarun baya.

 

A shekarar 2014, gwamnatin Barack Obama ta shirya taron kolin Amurka da kasashen Afirka karo na farko, inda ta dauki alkawura a gaban kasashen Afirka. Sai dai bayan taron, a maimakon ta kara samar da gudummawa, sai ta rage, har da kudaden da take samarwa a fannin yaki da cutar kanjamau a Afirka. A gun taron, Amurka ta kuma yi alkawarin zurfafa huldarta da kasashen Afirka da ma gudanar da taron a kai a kai, amma ba a sake yin taron ba har sai bayan tsawon shekaru 8. A karshen shekarar 2022, Amurka ta gudanar da taron karo na biyu, inda tsohon shugaban kasar Joe Biden ya yi alkawarin samar da iya abin da kasarsa take iya bayarwa don tabbatar da kyautata makomar Afirka, kuma a cewarsa zai kai ziyara Afirka a shekarar 2023, amma bai cika wannan alkawari ba sai zuwa karshen bara, lokacin da ya kusan sauka daga kujerar shugabanci, kuma ba mu san yaushe za a cika sauran alkawuran da ya dauka ba.

 

Bayan da gwamnati mai ci ta fara aiki, jerin matakan da ta dauka sun haifar da munanan illoli ga kasashen Afirka. In mun dauki misali da harajin kwastam na ramuwar gayya da ta dauka a baya bayan nan, inda ta sanya haraji mai yawa kan kasashen Afirka 51, ciki har da 50% a kan Lesotho da 47% a kan Madagascar da 40% a kan Mauritius, matakin da ya kasance tamkar yi wa kasashen fashi. Abin lura kuma shi ne, harajin ya dakatar da dokar samar da ci gaba da damammaki a Afirka da aka san ta da AGOA, tun kafin wa’adinta ya cika, lamarin da ya jefa kasashen Afirka da dama cikin mawuyacin hali wajen yin ciniki da Amurka.

 

Har kullum kasar Sin na ganin cewa, Afirka dandali ne na hadin gwiwar kasa da kasa, a maimakon wajen yin takara tsakanin manyan kasashe. Rashin girmamawa ne ga kasashen Afirka da al’ummarsu yadda Amurka take da rashin sanin nahiyar, kuma rashin sahihancin da take wa hadin gwiwarta da kasashen Afirka ya shaida gazarwata ta daukar kasashen Afirka da muhimmanci. Kasashen Afirka na bukatar kawaye na gaske. Idan gwamnatin Trump tana son samun karbuwa daga kasashen Afirka, dole ne ta gyara matsayinta, kuma ya kamata ta fara da fahimtar kowace kasa da ke nahiyar. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bom ya fashe a Barikin Sojoji na Giwa da ke Maiduguri
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi