Abin da ya sa na yi wa Buhari juyin mulki —Babangida
Published: 24th, February 2025 GMT
Tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (murabus) ya bayyana dalilin da ya hambarar da gwamnatin Janar Muhammadu Buhari a 1985.
Janar Babangida ya bayyana dalilin da gwamnatinsa ta karya darajar Naira da sauran sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ta yi bayan kifar da Buhari.
Babangida, wanda shi ne babban hafsan sojin kasa a lokacin Buhari, ya taka rawar gani a juyin mulkin da aka yi wa Shugaba Shehu Usman Shagari a 1983 da kuma na 1985 da ya kawo shi kan karagar mulki.
Ya ba da cikakken bayani game da abubuwan da suka faru a cikin littafin tarihin rayuwarsa da ya ƙaddamar a makon jiya.
Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar BiriLittafin na Babangida ya haifar da cece-kuce, game da muhimman batutuwan da suka dabaibaye mulkinsa na shekaru takwas, musamman soke zaben shugaban kasa na ranar 12 ga watan Yuni; kashe babban dan jarida, Dele Giwa; da kuma kashe Manjo Janar Mamman Vatsa bisa zargin yunkurin juyin mulki.
“Juyin mulkin 1985 ya zama dole.”A babi na shida, Babangida ya ba da hujjar juyin mulkin da aka yi wa Janar Buhari a 1985. Ya bayyana cewa juyin mulkin martani ga korafe-korafen ’yan Najeriya da kuma tabarbarewar al’amurana kasar.
Ya ce, “A farkon shekarar 1985, ’yan Najeriya sun fara fargaba game da makomar kasarmu. Al’amarin ya kasance mai hadari kuma yana cike da munanan alamun a fili da hatsarin da ke yanzu.
“A bayyane yake ga shugabancin sojojin cewa aikin da muka yi da nufin ceto ƙasarmu a shekarar 1983 ya watse,” kamar yadda Janar Babangida ya rubuta.
Ya ce rashin daukar mataki zai kawo rarrabuwar kawuna a tsakanin sojoji, wanda a ganinsa hakan zai haifar da mummunar illa ga kasar.
“Idan sojojin suka yi samu rabuwar kai, al’ummar za su bi sahu, kuma abin da zai biyo baya zai zama mai ban tsoro ne da ba za a iya tunani ba,” in ji shi.
A cewarsa, a shekarar 1983 sojoji sun hambarar da Shugaba Shagari ne cikin haɗin kai, amma sai aka fara samun rarrabuwar kawuna tsakaninsu.
“Sojoji, a matsayinsu na waɗanda aka sani da hadin kai, sai ga shi an fara samun guna-guni; down haka ya zama dole a yi wani abu don kada mu rasa kasar.
“Babban abin da na ji tsoro shi ne, rarrabuwar kawuna da ra’ayi a tsakanin sojoji na iya haifar da bangaranci a tsakaninsu. Idan kuma aka bari a ci gaba da samun gindin zama, to akwai hatsarin gaske.”
Ya zargi Buhari da mataimakinsa Birgediya Janar Tunde Idiagbon da mayar da mayar da sojoji saniyar ware, tare da daukar tsauraran matakan kama-karya wajen tafiyar da mulki.
“Sun dauki kansu kamar wasu waliyyai, inda suka kawo wa sojoji bakin jini a wurin al’ummar kasa. Suna take hakkin al’umma tare da cin zarafi babu kakkautawa,” in ji Babangida.
A cewarsa gwmanatin sojin Buhari ta yi mulki ne ta hanyar tsoratarwa maimakon sanya ’yan kyakkyawan fata a zukatan al’umma.
“Kamata ya yi mu Inganta rayuwarsu mu sa musu kyakkyawan fata cewa rayuwarsu za ta inganta. Amma maimakon haka sai aka yi ta kafa musu dokokin kama-karya.
“Sai aka wayi gari gwamnatin da aka kafa da niyyar cimma muradun bai-ɗaya na sojoji, ta koma ta wasu ’yan tsirarun mutane masu taurin kai,” in ji Babangida.
Taɓarɓarewar tattalin arzikiYa bayyana cewa tsarin musayar kaya na gargajiya da Buhari ya koma amfani da shi ya kara kassara tattalin arzikin Najeriya.
Ya ƙara da cewa lalacewar tattalin arziki da guna-gunin ’yan kasa kan matsin rayuwa na daga cikin abin da suka sa su hambarar da Buhari.
Ya ce, “Kamar yawancin juyin mulkin soja, mun yi ne sakamakon yawan korafe-korafen jama’a. Talakawa sun shiga matsanancin matsin rayuwa, ga shi yanayin tattalin arziki sai kara ta’azzara suke yi a kulla-yaumin.
“Kayayyakin masarufi da sauran bukatun yau da kullum sai karanci suke kara yi.
“Sannan ku a komawa amfani da tsohuwar hanyar yin ciniki ta hanyar musayar kaya a kasuwancin kasa da kasa yana nufin cewa ba a kama hanyar kawo karshen matsalolin tattalin arziki a tsakanin al’umma ba.
Dokokin kama-karya, sun tauye ’yancin walwalar jama’a, ga kuma hukunci mai tsauri, in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Buhari tattalin arziki Babangida ya
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
Babban daraktan kamfanin dillancin labaran kasar Qatar ya bayyana cewa taron gaggawa na kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da ke tafe yana nuni da wani muhimmin sauyi na hadin kan kasashen larabawa da musulmi dangane da laifukan da ake aikatawa kan al’ummar Palastinu.
A cewar Pars Today, dukkanin idanuwa a ranakun Lahadi da Litinin (15-16 ga Satumba, 2025) za su kasance a Doha, babban birnin kasar Qatar, wanda zai karbi bakuncin taron gaggawa na shugabannin kasashen Larabawa da na Islama, don ba da amsa ga baki daya kan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar.
Ana gudanar da wannan taron gaggawa ne a cikin yanayi na musamman na yanki da na duniya kuma ya biyo bayan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar. Ana dai kallonsa a matsayin wani gagarumin sauyi ba wai kawai dangane da batun Falasdinu ba, har ma da sauran ci gaban siyasa a yankin.
A cikin wannan mahallin, masana da kwararru kan harkokin yada labarai na Qatar sun jaddada cewa zaluncin da Isra’ila ke yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa tare da sake fasalin wasu muhimman batutuwan yankin.
Hadin kan Matsayin Larabawa da Musulunci
Ahmed Al-Rumaihi, Darakta-Janar na Kamfanin Dillancin Labarai na Qatar, ya ce hanyar shari’a ta kasa da kasa ita ce mafi kyawu kuma zabin da ya dace don tunkarar ci gaba da keta haddin ‘yan mamaya na (Sionist) – na farko daga cikin laifuffukan da aka rubuta da Benjamin Netanyahu, Firayim Ministan Isra’ila ya yi. Kotunan duniya, musamman kotun shari’a ta duniya, sun kafa sharuɗɗa da yawa waɗanda ke tabbatar da girman waɗannan laifuka.
Al-Rumaihi ya kara da cewa, ana ci gaba da yin Allah-wadai da wannan mugunyar ta’addancin da Isra’ila ke yi wa kasar Qatar, a duniya, kuma wannan ba wani abu ba ne, illa dai sakamakon yadda duniya ke kara wayar da kan jama’a game da keta haddin majalisar ministocin Isra’ila.
Farfado da Ra’ayin kishin Kasa
Babban editan jaridar Al-Sharq na kasar Qatar Jaber Al-Harami ya bayyana cewa, ha’incin da Isra’ila ta yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa zuwa wani mataki da ba a taba ganin irinsa ba, wanda ke karfafa imanin cewa ba kasa daya ba ce kawai, yankin gaba daya. Al-Harami ya jaddada cewa, Isra’ila ba ta amince da wani jan layi ba, ba ta bi yarjejeniyoyin da aka kulla ko yarjejeniya ba, a maimakon haka tana aiwatar da munanan manufofin ba tare da la’akari da ka’ida ba.
A cewar Al-Harami, ta hanyar wannan wuce gona da iri Isra’ila na neman kafa sabbin sharudda da bukatu a karkashin shirin da ake kira “Isra’ila Babba”, inda ta sanya kasashen Larabawa a gaban wani zabi na wanzuwa. Don haka wajibi ne taron na Doha ya tashi daga kace-nace zuwa aiki na hakika.
Hakazalika, Nasser Al-Azba, wani lauya na kasa da kasa, ya jaddada cewa, lokaci ya yi da ya wuce yin Allah wadai da take-take, maimakon daukar matakai masu amfani da kuma daukar matakai masu inganci a kasa.
Al-Azba ya bayyana cewa, harin da Isra’ila ta kai kan Qatar a baya-bayan nan, ya nuna karara karya ce ga yarjejeniyar Vienna ta 1968, wadda ta kafa tsarin doka na kare jami’an diflomasiyya da masu shiga tsakani na kasa da kasa. A tarihi, manzanni sun kasance suna samun cikakkiyar kariya, kuma wannan ka’ida tana cikin dokokin duniya a yau.
Lauyan dokar kasa da kasa ya kara da cewa mayar da martani bai kamata ya takaita ga matakan shari’a ba, amma kuma dole ne ya hada da kulla kawance da kasashe da ba na yammacin Turai ba kamar su China, Rasha, da kasashen BRICS, yayin da a lokaci guda za a tattara ra’ayoyin jama’a na duniya don fallasa irin ta’addancin Isra’ila.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci