Aminiya:
2025-05-01@03:45:11 GMT

HOTUNA: Yadda gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Kano

Published: 6th, February 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi a Ƙauyen Zago da ke Ƙaramar Hukumar Danbatta a Jihar Kano, ta ƙone gidaje, amfanin gona, da dabbobi, lamarin da ya janyo wa mazauna ƙauyen asara mai tarin yawa.

Gobarar, ta fara ne da safiyar ranar Laraba, inda ta ƙone gidaje da dama tare da lalata hatsi da sauran amfanin gona.

An yi garkuwa da tsohon Shugaban Hukumar NYSC Janar Tsiga Ɗan firamare ya je makaranta da bindiga yana barazanar harbe ɗalibai

Har ila yau, ta kashe shanu da sauran dabbobi mallakin mazauna ƙauyen.

Wasu daga cikin mazauna ƙauyen, Hayyo Zago da Abdulrahman Zago, sun ce gobarar ta ci gaba da ci har zuwa rana kafin jami’an kashe gobara su iss, inda suka yi nasarar kashe ta.

Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, Jami’in Yaɗa Labarai na Yanki, Abdullahi Musa Gyadi-Gyadi, ya ce za a fitar da cikakken bayani kan asarar da aka tafka daga baya.

A nasa ɓangaren, kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar ba.

Amma ana tattara cikakken rahoto kan lamarin.

 

Go hotunan yadda gobarar ta yi ɓarna a ƙauyen:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Ƙauye

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano

CP Bakori ya gode wa al’ummar Kano saboda goyon bayan da suke ba su a ƙoƙarin su na yaƙar masu aikata laifuka tare da kira ga ci gaba da haɗin kai wajen kai rahoton abubuwan da suke zargi ga Ƴansanda.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA