Aminiya:
2025-09-17@23:26:07 GMT

HOTUNA: Yadda gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Kano

Published: 6th, February 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi a Ƙauyen Zago da ke Ƙaramar Hukumar Danbatta a Jihar Kano, ta ƙone gidaje, amfanin gona, da dabbobi, lamarin da ya janyo wa mazauna ƙauyen asara mai tarin yawa.

Gobarar, ta fara ne da safiyar ranar Laraba, inda ta ƙone gidaje da dama tare da lalata hatsi da sauran amfanin gona.

An yi garkuwa da tsohon Shugaban Hukumar NYSC Janar Tsiga Ɗan firamare ya je makaranta da bindiga yana barazanar harbe ɗalibai

Har ila yau, ta kashe shanu da sauran dabbobi mallakin mazauna ƙauyen.

Wasu daga cikin mazauna ƙauyen, Hayyo Zago da Abdulrahman Zago, sun ce gobarar ta ci gaba da ci har zuwa rana kafin jami’an kashe gobara su iss, inda suka yi nasarar kashe ta.

Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, Jami’in Yaɗa Labarai na Yanki, Abdullahi Musa Gyadi-Gyadi, ya ce za a fitar da cikakken bayani kan asarar da aka tafka daga baya.

A nasa ɓangaren, kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar ba.

Amma ana tattara cikakken rahoto kan lamarin.

 

Go hotunan yadda gobarar ta yi ɓarna a ƙauyen:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Ƙauye

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.

 

Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.

Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.

NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa