An kashe wa ma’aurata ’ya’yansu uku a boye gawarsu a firinji
Published: 6th, February 2025 GMT
Wasu ma’aurata sun tsinci gawarwakin kananan ’ya’yansu uku a boye a cikin wani firinji a yankin Nnewichi da ke Nnewi a Jihar Anambra.
Iyayen yaran, Mista Udochukwu da Misis Chikazor Ejezie, sun tsinci gawar ’ya’yan nasu a cikin firinji ne bayan da suka dawo gida daga wurin aiki.
Bayan dawowarsu ne suka samu gidan a bude ba yadda suka saba ba, kasancewar yaran suka kulle gidan a duk lokacin da za su je wasa.
Da shigarma’auratan cikin gidan ne kuma suka ga gawarwakin yaran an sanya a cikin firinjin kayan kankara.
Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata Kotu ta ɗaure Farfesa shekara 3 kan aikata maguɗin zaɓeLamarin da ya faru a karshen mako ya tayar da kura, musamman a kafofin sada zumunta.
Bayan hakan ne gwamnatin jihar ta yi alkawarin bin diddigi tare da kama masu hannu a wannan aika-aika.
A yayin ziyarar da ta kai wurin, Kwamishinar Harkokin Mata da Walwalar Jama’a, Misis Ify Obinabo, ta ba da tabbacin yin duk mai yiwuwa wajen ganin an yi wa yaran adalci.
Kwamishinar, ta kuma jaddada haka a lokacin da ta ziyarci Asibitin Koyarwa na Jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke Nnewi, inda aka ajiye gawarwakin yaran.
Mazauna unguwar sun bayyana lamarin a matsayin babban tashin hankali a yayin da suke ta tausaya wa ma’auratan.
Tuni dai hukumomin jihar Anambra suka kaddamar da bincike kan lamarin da nufi lalubo bakin zaren.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Anambra kananan yara yara
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
Shugaba Bola Tinubu ya amince da naɗin Olumode Samuel Adeyemi a matsayin sabon Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa.
Sabon shugaban hukumar zai fara aiki a hukumance daga ranar 14 ga watan Agusta, 2025.
Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a BornoAn sanar da wannan naɗin ne a ranar Laraba cikin wata sanarwa da Hukumar CDCFIB, ta fitar, wacce sakatarenta, Abdulmalik Jibrin, ya rattaba wa hannu.
Wannan naɗin na zuwa ne bayan da shugaban hukumar na yanzu, Injiniya Abdulganiyu Jaji Olola, ke shirin ritaya a ranar 13 ga watan Agusta, 2025, bayan cika shekaru 60 a duniya.
Olumode Samuel Adeyemi yana da ƙwarewa da gogewa a aikin kashe gobara.
Ya fara aikinsa a Hukumar Kashe Gobara ta Abuja, kafin daga bisani ya koma Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa, inda ya bi matakai har ya kai matsayin Mataimakin Shugaban Hukumar a sashen kula da ma’aikata.
A tsawon lokacin da ya shafe yana aiki, ya samu horo da ƙwarewar da ake buƙata a cikin gida da kuma waje.
Haka kuma ya riƙe muƙamai daban-daban a hukumar, kuma memba ne a ƙungiyoyi irin su ANAN, Cibiyar Gudanar da Harkokin Kamfanoni ta Ƙasa, Cibiyar Gudanar da Harkokin Jama’a ta Ƙasa, da kuma Cibiyar Kula da Kuɗaɗe ta Ƙasa.
Hukumar ta yaba wa shugaban da zai ritaya, bisa gudunmawar da ya bayar da kuma irin shirye-shiryen da ya jagoranta a lokacin da yake shugabancin hukumar.