Aminiya:
2025-06-29@05:31:09 GMT

An ɗaure zawarawa a gidan yari kan aikata zina

Published: 31st, January 2025 GMT

Kotu ta daure wata matar aure da wani magidanci a gidan yari kan aikata lalata da juna.

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a Abuja ta yanke wa zawararwan hukuncin ɗaurin wata uku kowannensu ne bayan samun su laifin aikata zina da junansu.

Matar mai shekaru 25 da bazawarin mai shekara 30 sun amsa laifin a lokacin da aka karanta musu takardar tuhumar a gaban kotun.

Zawarawan sun kuma buƙaci kotun ta yi musu sassauci.

Da farko alƙalin ya ba da umarnin tsare su har sai sun kawo shaida da za su yi rantsuwa cewa su mutanen kirki ne, amma suka kasa.

Daga bisani Alƙali Olatunji Oladunmoye, ya yanke wa kowannensu hukuncin ɗaurin wata uku ko biyan tarar Naira 25,000.

Tun da farko, ɗan mai gabatar da ƙara, Dabo Yakubu, ya shaida wa kotu cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifin a jawabin da suka rubuta a caji ofis, bayan an kawo karar su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: bazawara bazawari matar aure

এছাড়াও পড়ুন:

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Masana da jami’ai a Nijeriya, sun yaba wa ci gaba na a-zo-a-gani da karin kuzarin da ake samu a hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Nijeriya, suna masu bayyana kokarin da aka yi zuwa yanzu a hadin gwiwar bangarorin biyu a tafarkin zamanantar da kansu.

Masanan sun bayyana haka ne yayin taro na biyu na bayan taron FOCAC da aka yi ranar Alhamis a Abuja, babban birnin kasar. Cibiyar nazarin dangantakar Sin da Afrika dake Nijeriya ce ta shirya taron mai taken “Hada Hannu Wajen Zamanantar da Sin da Afrika da cimma shirye-shirye 10 na Hadin Gwiwa a Cikin Al’ummar Sin da Afrika mai Makoma ta Bai Daya a Ko da Yaushe.”

Da yake jawabi, daraktan cibiyar nazarin Sheriff Ghali Ibrahim, ya ce daga Bandung a 1955 zuwa Beijing a 2024, Sin da Afrika sun ci gaba da bijirewa mulkin mallaka da danniya, yayin da Sin ta yi ta goyon bayan kasashen Afrika wajen zamanantar da kansu da samu ci gaba, ta hanyar zuba jari da bayar da tallafi da rance da sauransu.

Masu gabatar da jawabai da dama sun bayyana ci gaban da aka samu a baya-bayan nan a hadin gwiwar Sin da Nijeriya, suna masu jinjinawa hadin gwiwar abota bisa manyan tsare-tsare da shugabannin kasashen biyu suka cimma a bara. Sun kuma bukaci hukumomin Nijeriya su kyautata amfani da manufar soke haraji ta Sin, su kuma yayata damarmakin ci gaba da cimma burikan kasashen biyu na samun karin kuzari. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
  • An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
  • ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’
  •  Sojojin Isra’ila: Da Gangan Muke Kashe Faladinawa A Wurin Karbar Taimakon Abinci
  • Sarkin Zazzau ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
  • Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC
  • Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC
  • WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
  • Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
  • Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum