Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-02@17:09:43 GMT

Tarin Bola Na Haddasa Cutuka Ga Mazauna Tudun Ilu A Kaduna

Published: 28th, January 2025 GMT

Tarin Bola Na Haddasa Cutuka Ga Mazauna Tudun Ilu A Kaduna

Wani katafaren wurin zubar da shara da aka tanada a wajen Kaduna ya koma wata babbar sana’ar kasuwanci inda ‘yan gwangwan ke amfani da gurbataccen ruwan najasa domin amfanin Noma.

 

 

Wata Kungiyar ‘yan jarida ta ziyarci al’ummar Katanga da ke karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna inda aka fara gudanar da wannan aiki inda suka gano cewa kimanin ‘yan gwangwan 150 ne suka tsunduma kansu domin karfafa tattalin arziki a wurin da ake jibge sharar.

 

Jama’a na yin tururuwa zuwa wurin zubar da sharar na Katanga wanda shi ne babban wurin da gwamnatin jihar ta amince da sharar don tabbatar da tsaftar muhalli.

 

Mallam Zubairu shi ne shugaba, ya shaidawa tawagar ‘yan jarida da sauran kungiyoyin fararen hula da suka halarci wajen cewa sun fara gano wannan sana’ar ne mai riba fiye da shekaru 3 da suka wuce.

 

Ya ce suna samar da abin da bai gaza Naira 8,000 kullum, kuma suna biyan N1000 a matsayin haraji ga karamar hukumar.

 

Mallam Suleiman Kawosu, wanda ya yi tafiyar sama da Kilomita 70 daga Zariya zuwa wurin.

Ya ce yana sayar da wata motar dakon taki a kan kudi da bai gaza Naira 10,000 don ciyar da iyalansa masu ‘ya’ya 9 da kuma kula da su ba, kuma yana jin dadin wannan sana’ar.

 

A halin da ake ciki kuma tawagar daga baya ta koma Tudun Illu da ke karamar hukumar Kaduna ta Arewa, akwai wani katafaren rumbun da ake zubar da shara ba bisa ka’ida ba da ke da babbar kasuwa a cikin babban birnin jihar.

 

Da yake magana da tawagar, wani basarake a yankin Alhaji Bala Illu ya koka da cewa wurin da ba a amince da shi ba ya wanzu tsawon shekaru da dama kuma kwanan nan ya haddasa gobara a wata makarantar Firamare da ke kusa.

 

Don haka ya bukaci gwamnati ta dauki tsattsauran mataki ta hanyar share wurin tare da dakatar da masu aikata wannan aika-aika daga ayyukan da ba su dace ba.

 

Alhaji Shehu Usman ya tabbatar da abin da basaraken ya fada tun da farko sai dai ya kara da cewa mutane da dama a yankin sun kamu da rashin lafiya sakamakon illar muhalli da sharar ta haifar.

 

Masana yanayi irin su Gloria Kasang Bulus da Zinta Istifanus sun koka kan yadda ake samun juji a tsakiyar wuraren zama a Kaduna.

 

Ziyarar da ‘yan jarida da masu kula da muhalli suka yi ta rangadin wuraren zubar da ruwa na najasa ya kasance irinsa na farko don samun bayanai na farko kan batutuwan da suka shafi muhalli da sauyin yanayi domin su adana bayanansu da kuma bayar da rahoto ga masu iko kan bin kyawawan halaye na muhalli na duniya.

 

Cov/Shindong Bala/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: shara

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

Majiyar ta kara da cewa, bayan yunkurinsu bai yi nasara ba a Tsanyawa, maharan sun sake wani sabon shiri, inda suka kai hari a kauyen Yar Tsamiya da ke gundumar Faruruwa, karamar hukumar Shanono, da misalin karfe 1:30 na dare, inda suka kashe mutane uku suka, tare da sace wasu uku.

 

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori November 1, 2025 Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari