Kwamitin zaman lafiya da tsaro na Tarayyar Afirka ya sanar da cewa zai gudanar da zaman gaggawa yau Talata kan halin da ake ciki a gabashin Jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango (DRC).

Kwamitin na (PSC) zai gudanar da wani zaman gaggawa a yau Talata kan halin da ake ciki a yankin, wanda ke fama da yakin da ake yi tsakanin dakarun Kongo da mayakan M23″ in ji Paschal Chem-Langhee, mai magana da yawun kwamitin, yayin da al’amura ke kazanta a Goma, babban birnin gabashin DRC.

Kafin nan daruruwan ma’aikatan MDD da fararen hula a gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kongo sun tsere zuwa makociyar kasar, Rwanda, yayin da gomman sojojin Kongo din suka “mika wuya” ga jami’an tsaron Rwanda a ranar Litinin, bayan ‘yan tawayen M23 sun kwace iko da birnin na Goma mai muhimmanci a Kongo.

 ‘Yan tawayen na M23, waɗanda ake zargin suna samun goyon bayan Rwanda, sun zafafa hare-hare a gabashin Kongo a makon jiya, inda suka kwace muhimman birane, Sai dai Shugaban Rwanda Paul Kagame ya sha musanta zargin cewa yana goyon bayan ‘yan tawayen.

Shugaban Kenya William Ruto, wanda yake shugabancin kasashen Gabashin Afirka ya sanar a ranar Lahadi cewa, kungiyar za ta gudanar da wani taro na musamman a cikin sa’o’i 48 don tunkarar rikicin da yake yaduwa a Jamhuriyar Dimukuradiyar Kongo.

Ruto ya tabbatar da cewa tun da farko ya tattauna da Shugaban DRC Kongo Felix Tshisekedi da Shugaban Rwanda Paul Kagame, wadanda dukkansu suka amince za su halarci taron.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.

Shugaban marasa rinjaye na Majalisar Wakilai Ali Isah, ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na Majalisar bayan wata ganawa da mai kula da jihar Ribas Sole a Abuja.

 

Ali Isah, ya bayyana cewa mai kula da jihar ta Ribas ya kasance a gidan a wani bangare na ziyarar da ya saba yi domin yiwa kwamitin riko da ke sa ido kan al’amuran gwamnati.

 

Shugaban marasa rinjaye wanda ya jagoranci taron a madadin shugaban kwamitin wanda ya zama shugaban masu rinjaye na majalisar Farfesa Julius Ihonvere, ya bayyana gamsuwa da kokarin da mai gudanarwa shi kadai yake yi na wanzar da zaman lafiya a jihar.

 

Ya ce mai kula da jihar ya tuntubi manyan masu ruwa da tsaki kan rikicin shugabancin jihar Ribas, shugabannin cibiyoyin addini da na gargajiya, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki don ganin an warware matsalar cikin ruwan sanyi domin ci gaban jihar.

 

Sai dai jami’in da ya gabata, ya umurci mai kula da shi kadai da ya tabbatar da cewa rikicin shugabancin jihar Ribas bai shafi biyan albashin ma’aikatan gwamnati da wadanda suka yi ritaya duk wata da fansho ba kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da majalisar dokokin kasar ke yin duk mai yiwuwa don tabbatar da mulkin dimokuradiyya a kasar nan.

 

Ali Isah, ya kuma tabbatar da cewa kwamitin wucin gadi zai ci gaba da tuntubar mai gudanarwa da bangaren zartarwa don hana tsawaita dakatarwar daga wa’adin watanni shida domin samun ci gaba.

 

COV: TSIBIRI

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan