Kwamitin zaman lafiya da tsaro na Tarayyar Afirka ya sanar da cewa zai gudanar da zaman gaggawa yau Talata kan halin da ake ciki a gabashin Jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango (DRC).

Kwamitin na (PSC) zai gudanar da wani zaman gaggawa a yau Talata kan halin da ake ciki a yankin, wanda ke fama da yakin da ake yi tsakanin dakarun Kongo da mayakan M23″ in ji Paschal Chem-Langhee, mai magana da yawun kwamitin, yayin da al’amura ke kazanta a Goma, babban birnin gabashin DRC.

Kafin nan daruruwan ma’aikatan MDD da fararen hula a gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kongo sun tsere zuwa makociyar kasar, Rwanda, yayin da gomman sojojin Kongo din suka “mika wuya” ga jami’an tsaron Rwanda a ranar Litinin, bayan ‘yan tawayen M23 sun kwace iko da birnin na Goma mai muhimmanci a Kongo.

 ‘Yan tawayen na M23, waɗanda ake zargin suna samun goyon bayan Rwanda, sun zafafa hare-hare a gabashin Kongo a makon jiya, inda suka kwace muhimman birane, Sai dai Shugaban Rwanda Paul Kagame ya sha musanta zargin cewa yana goyon bayan ‘yan tawayen.

Shugaban Kenya William Ruto, wanda yake shugabancin kasashen Gabashin Afirka ya sanar a ranar Lahadi cewa, kungiyar za ta gudanar da wani taro na musamman a cikin sa’o’i 48 don tunkarar rikicin da yake yaduwa a Jamhuriyar Dimukuradiyar Kongo.

Ruto ya tabbatar da cewa tun da farko ya tattauna da Shugaban DRC Kongo Felix Tshisekedi da Shugaban Rwanda Paul Kagame, wadanda dukkansu suka amince za su halarci taron.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shi ma wasan da ta yi nasara a kan kungiyar Sifaniya a daf da za a tashi ta ci kwallon a gasar Zakarun Turai da na Newcastle United a Premier League. Tun daga nan alamomi suka fara bayyana cewar akwai tarin matsaloli a Liberpool, wadda kowanne wasa kwallo ke shiga ragarta in ban da wanda ta yi nasara a kan Arsenal 1-0 a Premier League cikin Agusta da wanda ta ci Burnley 1-0 a cikin watan Satumba a Premier League.

Sababbnin ‘Yanwasan da Liberpool ta saya a kakar banamages Giorgi Mamardashbili daga Balencia Jeremie Frimpong daga Bayern Leberkusen, Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen,

Milos Kerkez daga Bournemouth, Hugo Ekitike daga Eintracht Frankfurt, Aledander Isak daga Newcastle United, Armin Pecsi daga Puskas Akademia. Giobanni Leoni daga Parma Freddie Woodman daga Preston North, Will Wright daga Salford.

Wasu daga cikin matsalolin Liberpool A Yanzu

Matsalar masu buga mata tsakiya Liberpool ta samu sauye-sauye da yawa a fannin masu taka mata wasa daga tsakiya, bayan da wasu daga ciki suka bar kungiyar, ya dace a ce ta hada

fitattun da za ta fuskanci kakar bana.

Liberpool ta dauki Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen, amma har yanzu dan wasan bai nuna kansa ba, inda yake ta shan suka daga magoya bayan da suke ganin kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba.

Raunin ‘yanwasa da ke jinya

Raunin da wasu ‘yanwasan Liberpool suka ji sun taka rawar gani da kungiyar Liberpool ke kasa kokari a kakar nan. Daga ciki mai tsaron baya, Giobanni Leoni ya ji rauni a wasansa na farko a kungiyar, wanda ake cewa yana doguwar jinya. Mai tsaron raga Alisson Becker ya ji rauni a lokacin gasar zakarun turai wanda ake cewar zai yi jinya har karshen watan Oktoba, watakila ya wuce hakan.

Bayan Liberpool na yoyo

A kakar bara bayan Liberpool ya yi yoyo, duk da cewar kungiyar ce ta lashe kofin, amma dai an samu matsaloli da yawa a bayan. Kungiyoyi da dama sun amfana da kurakuren Liberpool a bara daga ciki har da Nottingham Forest da Brighton da kuma Brentford.

Wasu lokutan da zarar Liberpool ta kai kora sai kaga wagegen gibi tsakanin masu tsare baya da ‘yan tsakiya. Haka kuma tun kafin fara kakar bana, Liberpool ta buga wasannin atisaye, kuma tun a lokacin gurbin masu tsare baya ya nuna matasalar da kungiyar za ta iya fuskanta da fara

kakar nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025 Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari