Juyayin Shahadar Jagoran Shiriya Na Iyalan Gidan Manzon Allah Imam Ali Arridha {a.s} A Mash’had Sun Kai 3,500,000
Published: 24th, August 2025 GMT
Birnin Mashhad na Iran ya karbi bakwancin maziyarta 3,500,000 daga kasashe 20 a yayin taron tunawa da shahadar Imam Rida (a.s)
Dubban daruruwan masu Ziyara daga ciki da wajen kasar Iran ne suke gudanar da taron tunawa da zagayowar ranar shahadar Imam Ali dan Musa al-Rida (a.s) a birnin Mashhad mai alfarma da ke arewa maso gabashin kasar Iran.
Yayin da masu ziyarar suke ci gaba da isowa, ana gudanar da tarukan makoki a hubbaren da kuma titunan da ke kewaye da hubbaren Imam, inda taron jama’a ya kai kololuwa.
Dubban al’ummar Iran ne suka ci gaba da gudanar da isa hubbare daga sassa daban daban na kasar, daga tazarar daruruwan kilomita daga garuruwan su zuwa birnin Mashhad, a cikin yanayi mai tsauri, domin tunawa da wannan ranar domin juyayi.
An lullube birnin na Mashhad da bakaken kyalle tare da cika shi da alamun juyayi na tunawa da shahadar Jagora na takwas na Iyalan gidan Manzon Allah tsarkaka (a.s). dubun dubatan masu Ziyara ne suka yi tururuwa zuwa hubbaren Imam Riza (a.s) da ke wannan gari. Daruruwan mabiyan Iyalan gidan Jagora mai tausayi, Imamin shiriya Abu al-Hasan Ali dan Musa al-Rida (a.s) sun nufi haraminsa mai tsarki, wasu daga cikinsu sun yi tafiya mai nisa don nuna soyayyarsu ga wannan Imam mai girma.
Gwamnan birnin Mashhad mai tsarki ya ce: A yau sama da masu Ziyara sama da 3,500,000 daga kasashe 20 ne suka hallara a birnin Mashhad domin halartar tarukan juyayin ranar shahadar Imam Rida (a.s).
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jagora: Tunanin JMI Ta Yi ‘Biyayya Ga Amurka’ Ba Zai Taba Yiyuwa Ba. August 24, 2025 Masu Makoki A Mashad Sun Yi Cincirindo A Hubbaren Imam Reza (a) Da Ke Mashad August 24, 2025 Aragchi: Batun ‘Isra’ila Babba” Mafarki ne Kuma Barazana Ce Ga Zaman Lafiya A Duniya August 24, 2025 Dakarun IRGC A Inan Iran Sun Nuna Goyon Bayansu Ga Gwamnatin Iran August 24, 2025 Ma’aikatar Shari’a Ta Sojojin Kasar Iran Ta Ce; Dakarun ‘IRGC’ Barkono Ne A Idanun Makiya August 24, 2025 Makami Mai Linzamin Iran Kirar Qasim Basir Mafarkin Ban Tsoro Ne Ga Tsarin Tsaron Makiya August 24, 2025 Al’ummar Birnin Chicago Na Amurka Sun Gudanar Da Gagarumar Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa August 24, 2025 Kungiyar Hadin Kan Kasashen Musulmi Ta Bayyana Kakaba Yauwa A Gaza Da Laifin Yaki August 24, 2025 Ministan Tsaron Iran: Ba Mu Yi Amfani Da Manyann Makamanmu A Yaki Da Isra’ila Ba August 24, 2025 Holland: Karin ministoci 8 sun yi murabus saboda kin daukar matakai kan Isra’ila August 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Saboda wannan baiwa daga Allah, iyalai da ‘yan uwan mai akuyar suka sanar da shirye-shiryen gudanar da bikin murnar haihuwar ‘ya’yan akuyar a ranar Lahadi mai zuwa a Garun Dakasoye, karamar hukumar Garun Malam ta Jihar Kano, inda za a yi musu suna da kuma karatun Alkur’ani mai girma.
A nasa bangaren, mahaifin budurwar, Malam Aliyu dake Garin Dakasoye, ya tabbatar da cewa za su gudanar da bikin domin nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa wannan ni’ima da ya ba su.
Ya kara da cewa: “Mun gode wa Allah bisa wannan arziki, kuma muna sa ran gudanar da bikin tare da sanya musu suna domin nuna godiya ga Allah mai daukaka.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp