Aminiya:
2025-04-18@07:11:02 GMT

Abincin karnuka ya fi namu —Fursunonin Najeriya

Published: 14th, April 2025 GMT

Fursunoni a gidajen yarin daban-daban a sassan Najeriya sun koka game da munin irin abincin da ake ba su, wanda suka ce na karnuka ya fi shi.

Da dama daga cikin fursunonin da muka zanta da su sun bayyana cewa takwarorinsu sun sha mutuwa a sakamakon yunwa.

Wannan zargi na zuwa ne bayan da Hukumar Gidajen Yari ta Najeriya tare da wani kwamitin bincike mai zaman kansa sun ƙaryata zarge-zargen fursunonin kan yunwa a gidajen yari.

A watan Satumban 2024 ne Ministan Harkokin Cikin Gida,  Olubunmi Tunji-Ojo, ya kafa a kwamitin domin gudanar da bincike kan zargin jami’an gidajen yari da cin hanci da kuma cin zarafin fursunonin.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

Duk da cewa kwamitin ya tabbatar da zargin yunwa da fursunonin suka yi, Muƙaddashin Shugaban Hukumar Gidajen Yari ta Kasa, ya ce an zuzuta lamarin, saboda a cewarsa, babu alƙaluman da ke tabbatar da hakan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gidajen yari yunwa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kaddamar da wani babban kwamiti kan kidayar jama’a da gidaje mai zuwa, inda ya umurci mambobin su gabatar da rahoton farko cikin makonni uku.

Shugaban wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar sa, Femi Gbajabiamila, a wajen taron da aka gudanar a fadar gwamnati da ke Abuja, ya ce kidayar na da matukar muhimmanci ga ci gaban kasa da kuma tsare-tsare na gaskiya.

 

Ya lura cewa ingantaccen bayanan yawan jama’a yana da mahimmanci don yanke shawara mai inganci a cikin manyan sassan kamar kiwon lafiya, ilimi, tsaro, da kuma tsara tattalin arziki.

Shugaban ya jaddada cewa, an gudanar da kidayar jama’a ta karshe a shekarar 2006, wato kusan shekaru ashirin da suka wuce, kuma tun daga lokacin ne Najeriya ta fuskanci sauye-sauye a yawan al’umma, matsugunan jama’a, da kuma muhimman abubuwan da suka shafi kasa baki daya.

Ya kuma jaddada mahimmancin tsarin da aka yi amfani da shi na fasaha don tabbatar da sahihin sakamako mai inganci, inda ya bayyana bukatar yin hadin gwiwa a tsakanin dukkanin hukumomin da abin ya shafa, da suka hada da hukumar kidaya ta kasa, da hukumar kula da shaida ta kasa NIMC, da ma’aikatar kudi, da ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsare.

 

 

Shugaban kwamitin shugaban kasa kan kidayar jama’a da gidaje kuma ministan kasafin kudi da tsare-tsare, Sanata Atiku Bagudu, ya tabbatar da cewa kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin wa’adin makonni uku da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar.

 

Bello Wakili/Abuja

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas ta gabatar da shawara kan yarjejeniyar musayar fursunoni da tsagaita wuta
  • Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman
  • Dangote: Har yanzu gidajen mai ba su rage farashin mai ba
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa
  • Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwasta Gadar Mandafuma A Jihar Borno
  • Samarwa Matasa Abun Yi Shi Zai Kawo Ƙarshen Ta’addancin Boko Haram Da ‘Yan Bindiga – Zulum 
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Shirin Sakin Dukkanin Fursunonin Isra’ila Bisa Sharuddan Da Ta Gindaya
  • HOTUNA: Zulum ya karɓi baƙuncin Majalisar Sarakunan Arewa a Borno
  • An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya