Aminiya:
2025-09-17@23:13:22 GMT

’Yan bindiga sun mamaye mazaɓata —Ɗan majalisar Katsina 

Published: 19th, August 2025 GMT

A yayin zaman majalisar dokokin jihar Katsina, Babban Mai Tsawatarwa na majalisar, Hon. Ibrahim Umar Dikko, ya fashe da kuka a gaban takwarorinsa, yana bayyana yadda ’yan bindiga suka mamaye mafi yawan yankunan da ke cikin Ƙaramar Hukumar Matazu da yake wakilta.

Hon. Dikko ya bayyana cewa daga cikin gundumomi 10 da ke cikin Matazu, guda 8 sun faɗa hannun ’yan bindiga, inda ya ce manoma ba sa iya zuwa gonakinsu saboda tsoron harin da ake kai musu.

“A jiya da safe, a bakin garin kusa da makarantar sakandare, sun kashe wani matashi sannan suka sace shanu hudu da ake amfani da su wajen noma,” in ji shi cikin hawaye.

Ya kara da cewa a cikin kwanaki biyu da suka gabata, akalla manoma 12 aka kashe a gonakinsu.

Yadda bom ya kashe yara 2 ya jikkata wasu 6 a Borno Hisbah ta kama mutane 62 a cibiyar Gwamnatin Tarayya a Kano

“A jiya sun kashe manoma biyar a gonarsu. A ranar da ta gabata kuma sun kashe manoma bakwai. Wallahi, ba za a iya zuwa gona ba. Muna cikin mawuyacin hali, muna bukatar taimako,” in ji shi cikin murya mai sosa rai.

Wannan kukan da ɗan majalisar ya yi ya ƙara jaddada irin halin kunci da al’ummomin jihar Katsina ke ciki, musamman a yankunan da ke fama da hare-haren ’yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma.

An sace soja an kai hari a ƙauyuka 10 a Sakkwato

A wani lamari makamancin haka, rahotanni sun bayyana cewa mutane da dama sun mutu, ciki har da jami’ai hudu na hukumar tsaron al’umma na jihar, yayin da wasu da dama aka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato.

Harin da ake zargin wani shahararren shugaban ’yan bindiga mai suna Kallamu ya jagoranta — wanda ke da alaka da Bello Turji — ya shafi akalla kauyuka 10 daga ranar Laraba zuwa Asabar da ta gabata.

Kauyuƙan da aka kai wa hari sun hada da: Ɗan Tudu, Lafinge, Gidan Bature, Makuwana, Turtsawa, Garki, Faru, Najingi, da Zannan Bango.

“Sun kashe mutane da dama, sun sace wasu, sun kwashe fiye da shanu 100, sannan sun tare hanyar Yankasuwa zuwa Masawa inda suka sace matafiya,” in ji wani mazaunin yankin.

Galadiman Gobir, Alhaji Abubakar Sulaiman, ya tabbatar da mutuwar mutane 8 a kauyukan Dan Tudu da Makuwana, tare da sace mutane 50 a kauyuka daban-daban.

“Sun kai hari har sansanin sojoji a Dan Tudu, inda suka kashe soja daya da jami’an tsaro hudu. Har yanzu ba a tantance adadin wadanda aka sace ba,” in ji shi.

Wasu mazauna yankin sun ce an kai hare-hare sau biyu ko uku a wasu kauyuka cikin kwanaki hudu, lamarin da ya tilasta wa jama’a barin gidajensu.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Sakkwato, Ahmed Musa, ya tabbatar da harin da aka kai Makuwana da Gidan Bature, inda ya ce ya ziyarci Sabon Birni da Goronyo domin tantance lamarin da kuma jajanta wa iyalan da abin ya shafa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa Sakkwato Tsaro yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Mataimakinsa kan harkokin majalisa Honarabul Attahiru Danmadi ne ya wakilci dan majalisar ya kuma tabbatarwa wadanda lamarin ya shafa kokarinsa kan daukar matakan da suka kamata domin tabbatar da tsaron rayukan su da dawowa da zaman lafiya a yankunan.

 

Garuruwan da ‘yan bindigar suka tarwatsa a gundumar Kuchi sun hada da Fakku, sha’alwashi, tulluwa da Rafin- gora a inda mutane bakwai suka rasa rai. A gundumar Jabo kuwa kauyukan da lamarin ya shafa su ne; Gesolodi, Hilya, Guraye, Guma, Chakai, Modo, Badariya, Tafki, Balera, Gudumawa da Rafin shinka.

 

“Mun girgiza kwarai da wannan halin da kuke ciki. A matsayina na wakilin ku, zan ci-gaba da kokarin da ya kamata a majalisa domin ganin jami’an tsaro sun kawo karshen wannan ta’addancin.”

 

Dan Majalisar ya ce ya gabatar da bukata ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa domin tallafawa wadanda lamarin ya shafa kuma zai ci- gaba da bibiya domin ganin tallafin ya samu cikin lokaci.

 

Ya ce yana kokarin ganin rundunar sojoji ta kara tura wadatattun jami’ai tare da tallafa masu domin yakar ‘yan ta’addan da wanzar da zaman lafiya a yankunan.

 

Tallafin kayan abinci na gaggawa da dan majalisar ya bayar sun hada da buhuhuwan masara, gero, garin kwaki da kuma kuli- kuli.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000