Aminiya:
2025-11-02@17:09:50 GMT

’Yan bindiga sun mamaye mazaɓata —Ɗan majalisar Katsina 

Published: 19th, August 2025 GMT

A yayin zaman majalisar dokokin jihar Katsina, Babban Mai Tsawatarwa na majalisar, Hon. Ibrahim Umar Dikko, ya fashe da kuka a gaban takwarorinsa, yana bayyana yadda ’yan bindiga suka mamaye mafi yawan yankunan da ke cikin Ƙaramar Hukumar Matazu da yake wakilta.

Hon. Dikko ya bayyana cewa daga cikin gundumomi 10 da ke cikin Matazu, guda 8 sun faɗa hannun ’yan bindiga, inda ya ce manoma ba sa iya zuwa gonakinsu saboda tsoron harin da ake kai musu.

“A jiya da safe, a bakin garin kusa da makarantar sakandare, sun kashe wani matashi sannan suka sace shanu hudu da ake amfani da su wajen noma,” in ji shi cikin hawaye.

Ya kara da cewa a cikin kwanaki biyu da suka gabata, akalla manoma 12 aka kashe a gonakinsu.

Yadda bom ya kashe yara 2 ya jikkata wasu 6 a Borno Hisbah ta kama mutane 62 a cibiyar Gwamnatin Tarayya a Kano

“A jiya sun kashe manoma biyar a gonarsu. A ranar da ta gabata kuma sun kashe manoma bakwai. Wallahi, ba za a iya zuwa gona ba. Muna cikin mawuyacin hali, muna bukatar taimako,” in ji shi cikin murya mai sosa rai.

Wannan kukan da ɗan majalisar ya yi ya ƙara jaddada irin halin kunci da al’ummomin jihar Katsina ke ciki, musamman a yankunan da ke fama da hare-haren ’yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma.

An sace soja an kai hari a ƙauyuka 10 a Sakkwato

A wani lamari makamancin haka, rahotanni sun bayyana cewa mutane da dama sun mutu, ciki har da jami’ai hudu na hukumar tsaron al’umma na jihar, yayin da wasu da dama aka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato.

Harin da ake zargin wani shahararren shugaban ’yan bindiga mai suna Kallamu ya jagoranta — wanda ke da alaka da Bello Turji — ya shafi akalla kauyuka 10 daga ranar Laraba zuwa Asabar da ta gabata.

Kauyuƙan da aka kai wa hari sun hada da: Ɗan Tudu, Lafinge, Gidan Bature, Makuwana, Turtsawa, Garki, Faru, Najingi, da Zannan Bango.

“Sun kashe mutane da dama, sun sace wasu, sun kwashe fiye da shanu 100, sannan sun tare hanyar Yankasuwa zuwa Masawa inda suka sace matafiya,” in ji wani mazaunin yankin.

Galadiman Gobir, Alhaji Abubakar Sulaiman, ya tabbatar da mutuwar mutane 8 a kauyukan Dan Tudu da Makuwana, tare da sace mutane 50 a kauyuka daban-daban.

“Sun kai hari har sansanin sojoji a Dan Tudu, inda suka kashe soja daya da jami’an tsaro hudu. Har yanzu ba a tantance adadin wadanda aka sace ba,” in ji shi.

Wasu mazauna yankin sun ce an kai hare-hare sau biyu ko uku a wasu kauyuka cikin kwanaki hudu, lamarin da ya tilasta wa jama’a barin gidajensu.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Sakkwato, Ahmed Musa, ya tabbatar da harin da aka kai Makuwana da Gidan Bature, inda ya ce ya ziyarci Sabon Birni da Goronyo domin tantance lamarin da kuma jajanta wa iyalan da abin ya shafa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa Sakkwato Tsaro yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi

Gwamnatin Amurka ƙarƙashin Donald Trump ta sake sanya Najeriya cikin jerin “Ƙasashe Masu Matsala ta Musamman” saboda zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

Wannan zargi ya biyo bayan jawabin da Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya yi a taron Majalisar Ɗinkin Duniya a kwanan baya.

Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP

A lokacin taron Shettima ya bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin abin tausayawa, inda ya hi kira da a tabbatar da zaman lafiya ta hanyar kafa ƙasashe biyu masu zaman kansu.

Bayan jawabin nasa, wasu ƙungiyoyi suka fara yaɗa labarin cewa ana yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Najeriya, duk da cewa mutane da dama sun ƙaryata jita-jitar.

A ranar Juma’a, Trump ya wallafa wani rubutu a shafinsa na X, cewa Kiristoci na fuskantar barazana a Najeriya.

Ya yi iƙirarin cewar masu tsattsauran ra’ayi suna yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya .

Ya umarci ɗan Majalisar Amurka, Riley Moore da shugaban kwamitin kasafin kuɗi na Majalisar, Tom Cole, su binciki lamarin, sannan su gabatar masa da rahoto.

Shugaban ya ƙara da cewa ƙasarsa ba za ta zuba ido yayin da irin wannan “ta’addanci” ke faruwa a Najeriya da sauran ƙasashe ba.

Ya lashi takobin cewar Amurka za ta ci gaba da kare Kiristoci a duniya baki ɗaya.

Bayan wannan furuci, wasu sun zargi Trump da amfani da matsalar tsaron Najeriya don samun goyon bayan siyasa.

Har yanzu Gwamnatin Najeriya ba ta yi martani a kan lamarin ba, amma jami’an gwamnati a baya sun bayyana cewa rikice-rikicen da ake fama da su a ƙasar suna da nasaba da ayyukan ta’addanci, fashi, da rikicin ƙabilanci, ba addini ba.

Kalmar “Ƙasa Mai Matsala Ta Musamman” na nufin ƙasashen da Amurka ke ganin suna take haƙƙin ’yancin addini, kuma hakan na iya sa wa ta ƙaƙaba wa Najeriya takunkumai.

Idan ba a manta Najeriya ta fara shiga jerin irin waɗanda ƙasashe tun a shekarar 2020.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu