Matainakin shugaban kasar kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya bayyana cewa, daukewa Iran takunkuman zalunci wadanda kasashen yamma suka dora mata na daga cikin asalin hakkin kasar da aka tauye.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Aref yana fadar haka a jiya Asabar, ya kuma kara da cewa, kasar Iran ba zata manta da hakkin kasar wanda Amurka ta take tun farkon nasarar juyin juya halin kasar shekaru 46 zuwa yanzu ba, amma duk da haka sun bata damar tattaunawa.

 Yace: Muna son mu nunawa duniya kan cewa har yanzun muna hakuri, amma ba zamu taba manta da zaluncin da aka yi mana ba.   Mataimakin shugaban yana maganar ficewar kasar Amurka daga yarjeniyar JCPOA da kuma dorawa kasar takunkuman tattalin arziki mafi muni da nufin kifar da gwamnatin kasar. Yace dukkan takunkuman tattalin arzikin da gwamnatocin kasar Amurka ta dorawa kasar tun bayan nasarar juyin juya halin kasar shekaru 46 da suka gabata basa bisa ka’ida.  Mataimakin shugaban kasar yana fadar haka ne bayan da ministan harkokin wajen kasar Abbas Aragchi ya kammala zagaye na farko na tattaunawa ba kai tsaye ba kan shirin makamacin Nukliya na kasar da tokwaransa na kasar Amurka Steve Witkoff a kasar Omman tare da ministan harkokin wajen kasar Omman Badr Hamad Al-Busaidi a matsayin mai shiga tsakani.

Iran Ta Godewa Omman Da Shiryawa Da Kuma Gudanar Da Tattaunawa  Tsakanin Amurka Da Iran

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu tana aiwatar da shirye-shirye masu ɗaukar hankali ta hanyar manyan ayyukan gine-gine, shirye-shiryen tallafa wa matasa, da kuma sauye-sauye a fannonin noma, makamashi, ilimi da ƙere-ƙere.

 

Ministan ya bayyana cire tallafin fetur a matsayin ɗaya daga cikin manyan matakan da gwamnatin ta ɗauka domin farfaɗo da tattalin arziki.

 

Ya ce: “Ɗaya daga cikin manya kuma mafi tasiri daga cikin matakan da wannan gwamnati ta ɗauka shi ne cire tallafin fetur, wanda ko da yake ya kasance mai raɗaɗi, amma sauyi ne da ya zama dole. Bayan ceton tattalin arzikin ƙasa daga rugujewa, wannan mataki ya hana ɓarna da asarar kuɗi sosai a tattalin arzikin mu.”

 

A cewar sa, kuɗaɗen da aka ceto daga cire tallafin ana amfani da su ne wajen manyan ayyukan raya ƙasa irin su hanyar Legas zuwa Kalaba, hanyar Sakkwato zuwa Badagiri, shimfiɗa layin dogo na Kaduna zuwa Kano, da sake gina hanyar mota ta Abuja zuwa Kaduna da Kano.

 

Ya ƙara da cewa akwai cigaba da aka samu wajen saka hannun jari a fannin ayyukan jin daɗi a faɗin ƙasar nan, tare da ƙaruwa a cikin kuɗaɗen da ake tura wa jihohi a kowane wata, wanda ke ba su damar aiwatar da ayyuka masu tasiri a matakin jiha da ƙananan hukumomi.

 

Dangane da shirye-shiryen tallafa wa jama’a, Idris ya bayyana cewa sama da ƙananan harkokin kasuwanci 900,000 sun riga sun amfana daga Shirin Tallafi da Lamunin Shugaban Ƙasa, yayin da sama da ɗalibai 350,000 suke amfana da lamunin karatu domin tabbatar da cewa babu matashin da zai kasa karatu sakamakon rashin kuɗi.

 

Ya bayyana cewa gwamnati ta ware kimanin naira biliyan 70 don lamunin karatu, wanda sama da matasa 600,000 suke neman amfana da shirin.

 

Ministan ya kuma bayyana ƙirƙirar Hukummomin Cigaban Yankuna a faɗin ƙasar nan da cewa wani mataki ne da Shugaban Ƙasa Tinubu ya ɗauka domin tabbatar da cigaba bisa yanayin kowane yanki daga cikin yankunan siyasa shida na ƙasar nan.

 

Ya ce aikin bututun gas ɗin Ajakuta zuwa Kaduna da Kano (AKK) yana tafiya yadda ya kamata, kuma zai bai wa masana’antu da ke kan wannan hanya wutar lantarki domin farfaɗo da masana’antu.

 

Ya ce: “Da zarar an kammala aikin, zai kawo wutar lantarki daga Ajakuta zuwa Kaduna da Kano. Wannan yana nufin cewa dukkan masana’antun da ke kan wannan layi za a farfaɗo da su.”

 

Idris ya bayyana gwamnatin Tinubu a matsayin gwamnati mai ɗaukar rayuwar matasa da muhimmanci, inda ya ambaci shigar matasa da dama cikin Majalisar Zartarwa ta Tarayya a matsayin ministoci da kuma wasu muƙamai a hukumomin gwamnati.

 

Ya ƙara da cewa gwamnatin tana kashe naira biliyan 75 ta hanyar Bankin Masana’antu (BOI) domin tallafa wa ƙanana da matsakaitan masana’antu a fannoni daban-daban da nufin samar da ayyukan yi da kuma ƙarfafa matasa.

 

Ya ce: “Waɗannan ba wai wasu alƙaluma ne kawai marasa ma’ana ko maganganu na manufofi ba. Waɗannan damarmaki ne—damarmaki na zahiri, waɗanda za a iya auna su, ga kowane ɗan Nijeriya.”

 

Idris ya yi kira ga Kwamishinonin Yaɗa Labarai na jihohi da su ɗauki nauyin isar da saƙon da ya shafi manufofin gwamnati ga jama’a da kuma fahimtar yadda za su amfana da su.

 

Ya ce: “Saboda haka, nauyin mu ne a matsayin masu kula da yaɗa labarai, mu tabbatar da cewa ‘yan ƙasa a faɗin jihohin tarayya ba kawai sun san da waɗannan sauye-sauye da shirye-shirye ba ne, amma su ma fahimci yadda za su iya samun dama su amfana da su.”

 

Ya shawarci kwamishinonin da su koma jihohin su da sabon ƙwazo, su yi amfani da Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) da kuma haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki na cikin gida domin fassara shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya zuwa ayyuka masu amfani a matakin ƙasa.

 

Taron, wanda Gwamnatin Jihar Neja ta karɓi baƙuncin sa, ya haɗa kwamishinonin yaɗa labarai daga jihohin APC domin ƙarfafa dabarun sadarwa da kuma inganta haɗin gwiwa wajen aiwatar da Shirin Sabunta Fata a matakin jihohi da ƙananan hukumomi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tana Nazarin Sakon Amurka Na Bukatar Farfado Da Tattaunawa Shirin Makamashin Nukliya Na kasar
  • Iran Ta Yi Tir Da Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Dorawa Ma’aikaciyar MDD
  • 2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi
  • Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)
  • Aref Ya Bayyana Cewa: Iran Ba Ta San Kalmar Mika Wuya Ba A Al’adunta Da Tsaronta
  • Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
  • Aragchi: Kofar Iran Ta Tattaunawa A Bude Take, Amma Amurka Sai Ta Biya Kudade Kan Kura-Kuranta
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran