Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
Published: 13th, April 2025 GMT
Matainakin shugaban kasar kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya bayyana cewa, daukewa Iran takunkuman zalunci wadanda kasashen yamma suka dora mata na daga cikin asalin hakkin kasar da aka tauye.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Aref yana fadar haka a jiya Asabar, ya kuma kara da cewa, kasar Iran ba zata manta da hakkin kasar wanda Amurka ta take tun farkon nasarar juyin juya halin kasar shekaru 46 zuwa yanzu ba, amma duk da haka sun bata damar tattaunawa.
Iran Ta Godewa Omman Da Shiryawa Da Kuma Gudanar Da Tattaunawa Tsakanin Amurka Da Iran
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno
Wasu ’yan ta’adda da ake kyautata zaton ’yan Boko Haram ne sun kai hari a sabuwar unguwar Yamtake da ke Ƙaramar hukumar Gwoza a Jihar Borno, inda suka kashe sojoji biyu tare da wasu fararen hula da ba a bayyana adadinsu ba.
Majiyoyin tsaro da na cikin gida sun tabbatar da harin, inda suka ce maharan sun mamaye unguwannin ne da misalin ƙarfe 11:15 na daren Alhamis.
Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musammanƊaya daga cikin majiyar sojojin ta ce, kafin a aike da wata tawagar sojoji daga Gwoza, maharan sun riga sun afkawa jama’a da sansanin sojan Yamtake.
“Muna jiran tawagar masu ƙarfafa musu su dawo, amma mun sami labarin cewa mutane biyu daga cikin jami’anmu da wasu fararen hula harin ya shafe su. Ina ba da shawarar mu jira har sai sun dawo,” in ji shi.
Sai dai Sanata Ali Ndume, ya ce tun lokacin da lamarin ya faru yana tuntuɓar al’ummar unguwar Yamtake.
“Abin takaici ne cewa mutanenmu a ƙauyen Yamtake sun fuskanci mummunan harin Boko Haram a daren ranar Alhamis, ɗaya ne daga cikin unguwannin da suka karɓi ’yan gudun hijirar kwanan nan, gwamnatin Jihar Borno ta sake tsugunar da su.
“Abin baƙin ciki ne yadda sojoji biyu suka rasa ransu a bakin aiki, yayin da wasu fararen hula da ba a san ko su wanene ba na daga cikin waɗanda suka jikkata, Allah Ya gafarta musu.
“Amma kuma na yabawa Birgediya Janar Nasir Abdullahi, Birgediya Kwamanda na runduna ta 26 Task Force da jiga-jigan sojojinsa kan sadaukarwar da suka yi ba tare da ƙaƙƙautawa ba wajen daƙile hare-hare da dama, musamman waɗanda aka yi yunƙurin kaiwa farmakin a garin Gwoza.