Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
Published: 13th, April 2025 GMT
Matainakin shugaban kasar kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya bayyana cewa, daukewa Iran takunkuman zalunci wadanda kasashen yamma suka dora mata na daga cikin asalin hakkin kasar da aka tauye.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Aref yana fadar haka a jiya Asabar, ya kuma kara da cewa, kasar Iran ba zata manta da hakkin kasar wanda Amurka ta take tun farkon nasarar juyin juya halin kasar shekaru 46 zuwa yanzu ba, amma duk da haka sun bata damar tattaunawa.
Iran Ta Godewa Omman Da Shiryawa Da Kuma Gudanar Da Tattaunawa Tsakanin Amurka Da Iran
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci
Wata sabuwar badakala ta sake bata sunan kungiyar Tarayyar Turai, inda ‘yan sanda suka farmawa gidan toshuwar shugaban kula da manufofin harkokin wajen na kungiyar Federica Mogherini, tare da tsare ta a ranar Talata, a Belgium.
Mogherini wacce ta yi aiki a mukamin tun daga 2014 zuwa 2019, Ita da wasu abokan aikinta biyu ana binciken su kan yadda aka yi amfani da kudaden Tarayyar Turai ba bisa ka’ida ba, cin hanci da rashawa.
Federica Mogherini, jami’ar diflomasiyya ‘yar Italiya mai shekaru 52, ana tsare da ita tare da Stefano Sannino, babban jami’i a Hukumar da kuma mataimakin darakta na Kwalejin Turai.
An kama su, su ukun a wani bangare na binciken da Ofishin Mai Gabatar da Kara na Tarayyar Turai ya jagoranta.
Binciken ya shafi zargin nuna fifiko wajen bayar da shirin horo ga jami’an diflomasiyya.
Ofishin Mai Gabatar da Kara na Tarayyar Turai ya zarge su da “zamba wajen bayar da kwangilolin gwamnati, cin hanci da rashawa, inda ‘Yan sandan Belgium suka gudanar da jerin bincike a ranar Talata a hedikwatar Hukumar Kula da Harkokin Waje ta Tarayyar Turai, a gine-gine da dama na Kwalejin Turai da ke Bruges, da kuma gidajen wadanda ake zargin su uku uku.
Dama dai a cfen baya an gano tarin takardun kudi na Yuro a gidajen ‘yan majalisar dokoki na turai, tare da kyaututtuka daga Qatar, Mauritania, da Morocco. Lamarin da ya girgiza Majalisar Dokokin Turai matuka a watan Disamba na 2022. Ana zargin ‘yan majalisar wakilai da mataimakan majalisar dokoki da dama da karbar cin hanci da rashawa a madadin tasirinsu kan wasu shawarwari na majalisar.
Akwai wasu badakaloli da dama da ake yawan samu a cikin kasashen Turai, musamman game da karkatar da kudaden EU.
A cewar sabon rahoto daga Ofishin Mai Gabatar da Kara na Tarayyar Turai, amfani da kudaden EU ba bisa ka’ida ba ya zama ruwan dare a kasashe 27 na Tarayyar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu December 3, 2025 Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza December 3, 2025 Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta December 3, 2025 Kasar Qatar Ta Gargadi Isra’ila Game Da ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza December 3, 2025 Sharhi: HKI tana fama da karancin sojoji a dukkan rassan sojojin kasar December 2, 2025 Shugaba Pizishkiyan: Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufa December 2, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Janar Chiristopher Musa ( Ritaya) A Matsayin Ministan Tsaro December 2, 2025 Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa December 2, 2025 Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar Taka Su Da Mota December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci