Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

 

“Wannan babban shiri ne da zai sake fasalin Zamfara, ya tabbatar da ci gaba mai ɗorewa tare da inganta rayuwar al’umma,” inji shi.

 

Ya ƙara da cewa, a mafi yawan ƙananan hukumomin jihar ana gina sabbin hanyoyi na kilomita biyar a cikin birane, baya ga Gusau wadda ake gudanar da manyan ayyuka na musamman. Ya ce hakan zai rage cunkoso, ya haɗa al’umma, ya kuma farfaɗo da kasuwancin ƙauye da birane.

 

A fannin lafiya, gwamnati ta ƙaddamar da gina sabon babban asibiti a Nasarawa Burkullu a ƙaramar hukumar Bukkuyum, tare da sabunta cibiyoyin kiwon lafiya da dama a yankunan karkara, domin sauƙaƙa samun ingantaccen magani.

 

An kuma sanar da ci gaba da gyaran makarantu a dukkan ƙananan hukumomi, tare da samar da kujeru, littattafai, kayan koyo da horar da malamai domin tabbatar da ingantaccen ilimi ga yaran jihar.

 

Haka kuma, ana gina sabuwar kasuwa ta zamani a Nasarawa Burkullu, da ake sa ran za ta zama cibiyar bunƙasa sana’o’i da kasuwanci ga mazauna yankin. A bangaren ruwa da wutar lantarki kuwa, ana tono ruwan sha da kuma shimfiɗa sabbin hanyoyin rarraba wuta zuwa asibitoci, makarantun firamare da sakandare, da cibiyoyin gwamnati.

 

Dantawasa ya ce, an riga an kammala wasu daga ayyukan tare da ƙaddamar da su, yayin da sauran ke kan gaba, abin da ya tabbatar da cewa gwamnatin Lawal “ba ta tsaya kan magana kawai ba, tana aiki tare da sakamako a fili wanda jama’a ke iya gani da idonsu.”

 

“Wannan gwamnati ta tsayu kan gaskiya, amana, da samar da kyakkyawan sakamako ga al’umma. Ayyukan da ake gani su ne shaida,” inji Kwamishinan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i November 5, 2025 Labarai Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa November 5, 2025 Labarai Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
  • Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Qalibaf: Iran Da Pakistan Zasu Aiwatar Dukkan Yarjejeniyar Da Suka Cimma A Tsakaninsu
  • Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya
  • Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho
  • Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
  • Likitoci sun wayar da kan mata kan cutar Sankara a Gombe
  • Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka