Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka

Gwamnatin Tarayya ta ɗora alhakin dawowar hare-haren ta’addanci, ciki har da sace dalibai mata a jihar Kebbi da kai hari a coci a jihar Kwara, kan kalaman da Amurka ta yi kwanan nan a kan Najeriya.

Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya ce sakonnin da Shugaban Amurka Donald Trump ya wallafa, inda ya zargi Najeriya da “kisan kiyasin Kiristoci” tare da barazanar tura sojojin kasarsa, sun kara wa wasu ƙungiyoyin ’yan ta’adda kaimin kai hare-hare.

Babu addinin da ake yi wa kisan ƙare dangi a Binuwai — Gwamna Alia Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano

“Kalaman da Amurka ta yi kwanan nan sun kara wa wasu ƙungiyoyin masu tayar da kayar baya da ke son amfani da labaran ƙasashen waje kai hare-hare kan wuraren da ba su da kariya kaimi,” in ji Akume a ranar Laraba.

Yayin da yake magana kan yadda ta’addanci, hare-haren ’yan bindiga da matsalolin tsaro ke ci gaba da sauyawa a ƙasar, Sakataren Gwamnatin ya ƙara da cewa: “Kafin waɗannan kalaman, an riga an raunana ƙungiyoyin ta’addanci sosai, kuma sun rage kai kananan hare-haren daji. Wannan dawowa ya nuna muhimmancin haɗin gwiwa, ba wai Magana kawai ba, tsakanin Najeriya da Amurka.”

Trump, a jerin sakonnin da ya wallafa a shafin X tsakanin 30 ga watan Oktoba da 1 ga Nuwamba, 2025, ya ayyana Najeriya a matsayin “Ƙasa mai Matsala ta Musamman” saboda zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi.

Shugaban Amurka ya yi gargadin cewa zai iya tura sojojin Amurka zuwa Najeriya idan kisan da ake zargin bai tsaya ba.

Ya ce tuni ya umarci Ma’aikatar Yaƙi ta kasar da ta fara shirin yiwuwar daukar matakin soja idan tashin hankali ya ci gaba.

Trump ya kuma yi barazanar dakatar da dukkan taimakon Amurka ga Najeriya idan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta kasa magance abin da ya kira zaluntar Kiristoci.

A cikin jawabin da SGF ya yi a ranar Laraba, ya ce an riga an raunana cibiyoyin ta’addanci sosai kuma sun rage zuwa kananan hare-haren daji kafin waɗannan kalaman.

“Wasu ƙungiyoyi yanzu suna ƙoƙarin amfani da waɗannan kalaman don samun suna,” in ji shi.

Idan za a iya tunawa a cikin makon nan ne dai wasu ’yan bindiga suka sace dalibai 25 a makarantar sakandaren kwana ta GCGSS Maga da ke jihar Kebbi.

Kazalika, a cikin makon kuma ta wasu maharani sun farmaki wasu masu ibada a wani coci da ke Eruku a jihar Kwara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • Achraf Hakimi Ya Zama Gwarzon Wasan Kwallon Kafar Afirka Na Shekara Ta 2025
  • NAJERIYA A YAU: Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki
  • Wardley ya zama zakaran damben boksin na duniya
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: A Yanzu Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi
  • Nijar: An Dakatar Da Ayyukan Kungiyoyin Agaji Da Dama
  • Najeriya ta Fara tattaunawa da Amurka kan zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi
  • An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing
  • Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai