Ba kamar kayayyakin manyan kamfanoni irin su Ajinomoto, Bedan wadanda aka zuba su a cikin kwali, ana sayar da su cikin lafiyayyen mazubi kuma NAFDAC ta amince da su ba, wadannan danyun kaya ne da ba su da wata alama.

Babban abin ban tsoro shi ne ba za a iya gano masana’antunsu don bincikar sahihancinsu ba.

Da alama a yankin Arewacin Nijeriya din ake yin su amma an gaza gano hakan ko kuma an gano amma wa’alla saboda yawan bukatu an kasa dakilewa.

Bincike ya nuna cewa a kasuwar Singer da Abubakar Rimi da ke Kano, ana sayar da buhu mai nauyin kilo giram 25 na wannan sinadari kan Naira 45,000, wanda ke bai wa ‘yan kasuwa damar sayar da su a kanana wurare, ciki har da auna shi da abin da mazauna yankin ke kira ‘mudu’.

A manyan kasuwannin Kaduna da Maiduguri, kasuwar Sabon Gari da ke Sokoto, ana sayar da buhu mai nauyin kilogiram 25 a tsakanin Naira 46,000 zuwa Naira 50,000.

A cikin jaka mai nauyin kilo giram 25, ana iya samun kamar mudu ‘10 zuwa 15 ‘.

Abokan ciniki, ba tare da la’akari da hadarin dake tattare da kiwon lafiya ba, sun fi son wannan haramtaccen samfuri saboda yawan abin da za su samu daga mudu da kuma saukin yin almundahana ta hanyar cakuda shi da gishiri don kara yawansa da samun riba.

A kwanakin baya ne hukumar ta NAFDAC ta rufe wani dakin ajiyar kaya na kamfanin ‘DEE-LITE IMPED Distribution Co. Ltd’ da ke Jihar Sokoto, bayan ta gano wani adadi mai yawa na kayan abinci marasa rajista da suka hada da buhu 5,347 na MSG.

Rumbun ajiyar da ke kan titin Coca-Cola, daura da Western Bypass a Sokoto, an gano ya saba wa ka’idojin hukumar NAFDAC. A cewar hukumar ta NAFDAC, kamfanin ya shigo da haramtaccen samfurin MSG babu izini a karkashin takardar izinin sarrafawa amma an same shi yana sayar da samfurin kai tsaye, wanda haramun ne kuma yana da hadari ga lafiyar dan’Adam.

Wani masani kan harkokin kiwon lafiya da ke zaune a Gombe, Dokta Abdullahi Guruji ya ce ya kamata masu amfani da su su yi hattara da abubuwan da suke amfani da su domin gujewa duk wata matsala a fannin lafiya. Guruji ya ce ya zama wajibi masu amfani da su daina sadaukar da lafiyarsu a kan burin farashin kayan abinci masu arha.

A cewarsa, bai kamata a ce alhakin kare lafiyar mutum ya takaita ga hukumar NAFDAC da SON da sauran hukumomi kadai ba. Ya bukaci kowane dan Nijeriya da ya kula da kansa da kuma sauran ‘yan kasarsa domin kaucewa wannan hatsarin da ke kunno kai a harkar lafiya.

A yayin da yake kira ga masu sayar da abinci da su taka rawar gani a wannan fanni, ya bukace su da su kula da lafiyar kwastomominsu ta hanyar yin amfani da ingantattun kayayyakin dafa abinci.

Sai dai kwarare a fannin lafiyar ya dora wa hukumar ta NAFDAC alhakin kara kaimi a fannin tabbatar da doka da oda inda ya ce yin hakan zai dakile ayyukan marasa kishin Nijeriya da suke jajircewa wajen cutar da ‘yan Nijeriya.

“Duk lokacin da muka ziyarci kasuwa, za mu ceci mutane da yawa daga matsalolin kiwon lafiya ta hanyar rufe shagunan masu sayar da monosodium glutamate, masu sayar da magungunan jabu / marasa inganci, da masu siyar da abubuwan sha masu dandano, na cikin kwalba a cikin sauran abubuwan da ke zama abin sha,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Hadari Kasuwanni Lafiya ana sayar da

এছাড়াও পড়ুন:

UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon

Wani mai magana da yawun rundunar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya (UNIFIL) ya tabbatar da cewa Isra’ila ta gina katanga kan iyakar da ta ratsa zuwa cikin yankin kasar Lebanon kusa da garin Yaroun, abin da tawagar ta bayyana a matsayin keta kudurin Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya mai lamba 1701.

“Isra’ila ta shafe shekaru da dama tana gina katanga a gefen Layin da aka Shata da ya raba yankunan Falastinu da Isra’ila ta mamaye da Lebanon, amma a cikin wannan yanayi katangar Isra’ila ta ratsa layin da ya raba bangarorin biyu,” in ji mai magana da yawun UNIFIL. “Don haka muna nuna rashin amincewa da wannan mataki, Wannan, a bayyane ya keta kuduri mai lamba 1701 da kuma hurumin kasar  Lebanon.” Inji shi.

Dakarun Masu Sanya ido kan zaman lafiya a kudancin kasar Lebanon UNIFIL  sun yi nazarin wurin kuma kuma tabbatar da cewa katangar ta ketare Layin da aka shata.

A cewar UNIFIL,  sun gano cewa katangar tana cikin kasar Lebanon kuma ta  kai  kimanin mita murabba’i 4,000 a cikin kasar Lebanon”.  Mai magana da yawun rundunar ya kara da cewa, tawagar ta sanar da sojojin na Isra’ila a hukumance  game da keta dokar da suka yi, inda suka mayar da martanin cewa za su dubi lamarin.

UNIFIL ta jaddada cewa za ta ci gaba da bin diddigin lamarin, da kuma ci gaba da Magana tare da dukkan bangarorin da abin ya shafa don tabbatar da cewa an kiyaye doka da kuma yin aiki da kudiri mai lamba 1701.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Zanga-Zangar Lumana November 26, 2025 Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu November 26, 2025 Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta November 26, 2025 EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru  Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa
  • Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro
  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kwara Ta Sanar da Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajjin 2026