Ba kamar kayayyakin manyan kamfanoni irin su Ajinomoto, Bedan wadanda aka zuba su a cikin kwali, ana sayar da su cikin lafiyayyen mazubi kuma NAFDAC ta amince da su ba, wadannan danyun kaya ne da ba su da wata alama.

Babban abin ban tsoro shi ne ba za a iya gano masana’antunsu don bincikar sahihancinsu ba.

Da alama a yankin Arewacin Nijeriya din ake yin su amma an gaza gano hakan ko kuma an gano amma wa’alla saboda yawan bukatu an kasa dakilewa.

Bincike ya nuna cewa a kasuwar Singer da Abubakar Rimi da ke Kano, ana sayar da buhu mai nauyin kilo giram 25 na wannan sinadari kan Naira 45,000, wanda ke bai wa ‘yan kasuwa damar sayar da su a kanana wurare, ciki har da auna shi da abin da mazauna yankin ke kira ‘mudu’.

A manyan kasuwannin Kaduna da Maiduguri, kasuwar Sabon Gari da ke Sokoto, ana sayar da buhu mai nauyin kilogiram 25 a tsakanin Naira 46,000 zuwa Naira 50,000.

A cikin jaka mai nauyin kilo giram 25, ana iya samun kamar mudu ‘10 zuwa 15 ‘.

Abokan ciniki, ba tare da la’akari da hadarin dake tattare da kiwon lafiya ba, sun fi son wannan haramtaccen samfuri saboda yawan abin da za su samu daga mudu da kuma saukin yin almundahana ta hanyar cakuda shi da gishiri don kara yawansa da samun riba.

A kwanakin baya ne hukumar ta NAFDAC ta rufe wani dakin ajiyar kaya na kamfanin ‘DEE-LITE IMPED Distribution Co. Ltd’ da ke Jihar Sokoto, bayan ta gano wani adadi mai yawa na kayan abinci marasa rajista da suka hada da buhu 5,347 na MSG.

Rumbun ajiyar da ke kan titin Coca-Cola, daura da Western Bypass a Sokoto, an gano ya saba wa ka’idojin hukumar NAFDAC. A cewar hukumar ta NAFDAC, kamfanin ya shigo da haramtaccen samfurin MSG babu izini a karkashin takardar izinin sarrafawa amma an same shi yana sayar da samfurin kai tsaye, wanda haramun ne kuma yana da hadari ga lafiyar dan’Adam.

Wani masani kan harkokin kiwon lafiya da ke zaune a Gombe, Dokta Abdullahi Guruji ya ce ya kamata masu amfani da su su yi hattara da abubuwan da suke amfani da su domin gujewa duk wata matsala a fannin lafiya. Guruji ya ce ya zama wajibi masu amfani da su daina sadaukar da lafiyarsu a kan burin farashin kayan abinci masu arha.

A cewarsa, bai kamata a ce alhakin kare lafiyar mutum ya takaita ga hukumar NAFDAC da SON da sauran hukumomi kadai ba. Ya bukaci kowane dan Nijeriya da ya kula da kansa da kuma sauran ‘yan kasarsa domin kaucewa wannan hatsarin da ke kunno kai a harkar lafiya.

A yayin da yake kira ga masu sayar da abinci da su taka rawar gani a wannan fanni, ya bukace su da su kula da lafiyar kwastomominsu ta hanyar yin amfani da ingantattun kayayyakin dafa abinci.

Sai dai kwarare a fannin lafiyar ya dora wa hukumar ta NAFDAC alhakin kara kaimi a fannin tabbatar da doka da oda inda ya ce yin hakan zai dakile ayyukan marasa kishin Nijeriya da suke jajircewa wajen cutar da ‘yan Nijeriya.

“Duk lokacin da muka ziyarci kasuwa, za mu ceci mutane da yawa daga matsalolin kiwon lafiya ta hanyar rufe shagunan masu sayar da monosodium glutamate, masu sayar da magungunan jabu / marasa inganci, da masu siyar da abubuwan sha masu dandano, na cikin kwalba a cikin sauran abubuwan da ke zama abin sha,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Hadari Kasuwanni Lafiya ana sayar da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato

Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, ya ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani guda 20, tare da riguna ruwa (life jackets) 2,000, domin rage haɗurran da ke aukuwa sakamakon ambaliya da nutsewar jirage a sassan jihar.

An ƙaddamar da jiragen ne a ƙaramar hukumar Wamakko a ranar Laraba, inda gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin shirin gaggawa na tallafa wa al’ummar da ke fama da illar ambaliya da haɗurra a ruwa.

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB

“Mun dauki wannan mataki bayan rahotannin da muke samu na yawaitar hatsarurruka da rasa rayuka da dukiya sakamakon jiragen katako da mutane ke amfani da su,” in ji Gwamna Ahmad Aliyu.

Gwamnan ya miƙa godiya ga shugabar hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), Hajiya Zubaida Umar, bisa hadin kai da goyon bayan da hukumar ke bayarwa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiya, tare da inganta ayyukan ceto da agaji a jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, an horar da direbobin jiragen ruwan da za su riƙa kula da su, kafin a raba su zuwa ƙananan hukumomi goma (10) da suka fi fuskantar barazanar ambaliya da suka haɗa da: Goronyo, Shagari, Sabon-Birni, Wurno, Rabah, Wamakko, Silame, Kebbe, Tambuwal da Isa.

Gwamnan ya kuma yi gargaɗin cewa za a hukunta duk wani da ya ɗauki lodi fiye da ƙima a cikin jiragen, yana mai cewa “wannan jirage da rigar ruwa na jama’a ne, kuma wajibi ne shugabannin ƙananan hukumomi su tabbatar da kula da su yadda ya kamata.”

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankunan da za a rabawa jiragen sun bayyana ra’ayinsu dangane da lamarin, inda wani Tanimu Goronyo, daga karamar hukumar Goronyo, ya ce: “Gwamnatin Sakkwato ta kauce hanya.

“Abin da muke bukata a yanzu shi ne hanyoyin mota da magudanan ruwa. Ambaliya tana mamaye yankunan mu ne saboda babu hanya. Idan gwamnati ta kashe wannan kuɗi wajen gina hanya, sai an fi cin moriya.”

Shi ma wani Muhammad Kabiru, daga Silame, ya bayyana farin cikinsa da sayen jiragen, sai dai ya roƙi gwamnati da ta mai da hankali wajen gina hanyoyin mota saboda abin da suka fi buƙata ke nan.

“Mu a Silame jirgi yana da amfani, amma hanyar mota ita ce babbar buƙatar mu. Idan aka samar da ita, ambaliya ba za ta hana mu zirga-zirga ba.”

Yayin da gwamnatin Sakkwato ke ɗaukar matakan gaggawa don rage hatsarurruka da ambaliya ke haifarwa, al’umma na ci gaba da neman tsarin da zai magance tushen matsalar – musamman samar da ingantattun hanyoyi da magudanan ruwa a karkara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin