Idan masu ajiya a Bnkin suka ajiye akalla Naira 10,000 a Asusun ajiya na Bankin ko kuma a cikin Lalitar ajiyarsu ta Bankin a kalla a cikin kwanuka 30, hakan ya nuna cewa, sun tsallake zamowa Zakarun samun damar lashe kyaututuka a wata daya, inda kuma za su shiga gasar zagaye ta karashe.

Kazalika, a cikin kowanne wata daya, mai ajiyar zai iya zamaowa a cikin rukunin Zakaru 70, inda kowanne mai ajiya daya a Bankin, zai iya karbar Naira 100,000.

Har ila yau, a cikin watanni uku kuma, kowanne mai ajiya daya a Bankin na Stanbic IBTC, da ya fito daga yanki bakwai da ake yin kasuwanci, zai lashe Naira miliyan daya, inda kuma a zagayen gasar na karashe ta zango, wanda ya samu nasara, zai iya lashe Naira miliyan biyu.

Bugu da kari, a zagayen karshe da za a karkare,  wanda suka zamo Zakaru. Kowannen su, zai samu Naira miliyan biyar.

Bankin na Stanbic IBTC, ya shafe sama da shekaru uku, yana yana sakawa masu ajiya da Bankin, inda ya zuwa yanzu, sama da masu ajiya da Bankin miliyan 1,900 suka samu nasaraa karkashin tsarin sa na, Reward4Sabing Promo 4.0.

Kazalika, Bankin ya rabarwa da wadanda suka samu nasara  jimlar  kyututukan kudade, da suka kai miliyan 318.

A saboda da irin wannan garabasar ta Bankin, yana da kyau daga yau ka fara tunanin fara yin ajiya a Bankin na Stanbic IBTC Bank.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Muna so a kafa doka ta bincikar yadda ’yan Nijeriya ke tara dukiya — EFCC

Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arziki ta’annati a Nijeriya ta buƙaci Majalisar Tarayyar da ta amince da ƙudirin dokar da zai ba ta damar bincikar ɗaiɗaikun ’yan Najeriya game da yadda suka tara dukiyarsu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito Shugaban EFCC, Ola Olukayode yana cewa ƙudirin mai suna “Unexplained Wealth Bill” ya je gaban ’yan majalisar tun a majalisa ta tara, wanda suka yi watsi da shi.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 24 a Arewa maso Gabashin Nijeriya An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba

“Akwai alaƙa mai ƙarfi tsakanin ɓarnar da ake yi arzikin ƙasarmu da kuma matsalar tsaro,” a cewarsa yayin wani taro da kwamatocin majalisar tarayya suka shirya kan arzikin ƙasa.

“Idan kana bincikar ayyukan ’yan fashin daji, da ta’addanci, za ka ga suna da alaƙa da wani nau’i na cin hanci da rashawa, ko kuma karkatar da kuɗaɗen da suka kamata a yi wa al’umma aiki.

“Ina neman ku taimaka min wajen amincewa da ƙudirin “Unexplained Wealth Bill”. Shekara ɗaya kenan ina neman hakan, kuma shi ne dai majalisa ta tara ta yi watsi da shi. “Idan ba mu binciki dukiyar da mutane suka tara ba ba za mu taɓa gyara al’amuran ba.

“Akwai wani da ya yi aiki shekara a wata ma’aikata. Mun lissafa baki ɗayan albashi da alawus ɗinsa. Sai kuma muka gano gidaje biyar da yake da su, biyu a Maitama, uku a Asokoro. Amma kuma ana so mu gabatar wa kotu hujja a kansa kafin mu yi wani bincike. Wannan abin takaici ne.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • “Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
  • Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa
  • Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga
  • Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
  • Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
  • Muna so a kafa doka ta bincikar yadda ’yan Nijeriya ke tara dukiya — EFCC
  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha
  • An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025
  • Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal