Sanata Oluremi Tinubu yt gana da sarakunan Taraba, ta kuma ba da gudummawar naira miliyan 50 don tallafa wa mata 1,000, da kayan aiki dubu 10,000 ga ma’aikatan lafiya

 

Uwargidan shugaban Najeriya, Sanata Oluremi Bola Ahmed Tinubu, ta bukaci shugabannin gargajiya da su marawa shirin ta na sabon fata ta hanyar wayar da kan jama’a game da shirye-shiryen kiwon lafiya da ke gudana a fadin kasar.

 

Misis Tinubu ta yi wannan roko ne a Jalingo, babban birnin jihar Taraba, yayin wata ganawa da sarakunan gargajiya a ranar Alhamis, wanda aka gudanar a dakin taro na uwargidan gwamnan jihar.

 

Uwargidan shugaban kasa, Sen. Oluremi Bola Ahmed Tinubu da ta isa filin jirgin saman Danbaba Suntai a ranar Alhamis da tsakar rana, ta samu tarba daga gwamna Agbu Kefas da matarsa, Misis Agyin Kefas tare da manyan jami’an gwamnati, da kuma dimbin magoya bayan jam’iyyar PDP mai mulki a jihar da kuma babbar jam’iyyar adawa ta APC.

 

Mrs Tinubu ta kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu a jihar Taraba, tare da rakiyar uwargidan mataimakin shugaban kasa, Hajiya Nana Kashim Shettima, ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammed Ali Pate, da babban daraktan hukumar kula da lafiya matakin farko na kasa Dr Muyi Aina da dai sauransu.

 

Ziyarar ta na kuma da nufin karfafa gwiwar ma’aikatan kiwon lafiya na sahun gaba ta hanyar ba da tallafi da kuma sanin irin kokarin da suke yi, da kuma wayar da kan jama’a game da cutar kanjamau, musamman yaduwar cutar kanjamau daga uwa zuwa ’ya’ya.

 

Da take jawabi a yayin ganawarta da shugabannin gargajiya, Sen. Oluremi Tinubu, ta bayyana cewa hada kai da sarakunan gargajiya zai taimaka wa gwamnatin tarayya wajen isar da sako game da samarwa da kuma maganin cutar kanjamau da tarin fuka kyauta, inda ta bayyana muhimmiyar rawar da suke takawa wajen hada kan jama’a.

 

Da yake mayar da jawabi, Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Taraba kuma Aku Uka na Wukari, HRM Manu Ishaku Adda Ali, ya bayyana ziyarar Misis Tinubu a matsayin alheri ga jihar.

 

Sai dai Sanata Oluremi Tinubu, jim kadan bayan ganawarta da shugabannin gargajiya, ta zarce zuwa filin wasa na Jolly Nyame, inda ta kaddamar da rabon kayayyakin sana’o’in ga ungozoma a fadin yankin Arewa maso Gabas.

 

A nata jawabin, ta kuma jaddada kudirin gwamnatin tarayya na samar da ayyukan kiwon lafiya da nufin rage mace-macen mata da kananan yara a fadin kasar nan.

 

A nasa jawabin, Ministan Lafiya, Farfesa Ali Pate, ya ce a yankin Arewa maso Gabas kadai, an horar da ma’aikatan kiwon lafiya 8,500, daga cikinsu 1,300 daga jihar Taraba.

 

A cewarsa, sama da cibiyoyin kiwon lafiya 1,000 ne ke samun tallafi a duk shekara daga asusun samar da kiwon lafiyai, ciki har da 170 a jihar.

 

Gwamna Agbu Kefas ya yabawa uwargidan shugaban kasar bisa wannan karimcin, inda ya ce jihar ta yi tarayya cikin hangen nesa na shirin sabunta fata.

 

A nata bangaren, uwargidan gwamnan, Misis Agyin Kefas, ita ma ta nuna jin dadin ta bisa yadda aka yi musu dauki, sannan ta yabawa ministan lafiya da walwalar jama’a bisa jajircewar sa.

 

A halin da ake ciki, Sanata Oluremi Tinubu ya mika kayan sana’o’in hannu guda 10,000 ga ungozoma a fadin jihohin Arewa maso Gabas shida, sannan ta mika chekin kudi naira miliyan 50 domin tallafa wa mata 1,000 a jihar Taraba.

 

 

Sani Sulaiman

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taraba uwargidan shugaban jihar Taraba kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe

Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.

Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.

Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno

Da yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.

“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.

A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.

Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago