Sanata Oluremi Tinubu yt gana da sarakunan Taraba, ta kuma ba da gudummawar naira miliyan 50 don tallafa wa mata 1,000, da kayan aiki dubu 10,000 ga ma’aikatan lafiya

 

Uwargidan shugaban Najeriya, Sanata Oluremi Bola Ahmed Tinubu, ta bukaci shugabannin gargajiya da su marawa shirin ta na sabon fata ta hanyar wayar da kan jama’a game da shirye-shiryen kiwon lafiya da ke gudana a fadin kasar.

 

Misis Tinubu ta yi wannan roko ne a Jalingo, babban birnin jihar Taraba, yayin wata ganawa da sarakunan gargajiya a ranar Alhamis, wanda aka gudanar a dakin taro na uwargidan gwamnan jihar.

 

Uwargidan shugaban kasa, Sen. Oluremi Bola Ahmed Tinubu da ta isa filin jirgin saman Danbaba Suntai a ranar Alhamis da tsakar rana, ta samu tarba daga gwamna Agbu Kefas da matarsa, Misis Agyin Kefas tare da manyan jami’an gwamnati, da kuma dimbin magoya bayan jam’iyyar PDP mai mulki a jihar da kuma babbar jam’iyyar adawa ta APC.

 

Mrs Tinubu ta kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu a jihar Taraba, tare da rakiyar uwargidan mataimakin shugaban kasa, Hajiya Nana Kashim Shettima, ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammed Ali Pate, da babban daraktan hukumar kula da lafiya matakin farko na kasa Dr Muyi Aina da dai sauransu.

 

Ziyarar ta na kuma da nufin karfafa gwiwar ma’aikatan kiwon lafiya na sahun gaba ta hanyar ba da tallafi da kuma sanin irin kokarin da suke yi, da kuma wayar da kan jama’a game da cutar kanjamau, musamman yaduwar cutar kanjamau daga uwa zuwa ’ya’ya.

 

Da take jawabi a yayin ganawarta da shugabannin gargajiya, Sen. Oluremi Tinubu, ta bayyana cewa hada kai da sarakunan gargajiya zai taimaka wa gwamnatin tarayya wajen isar da sako game da samarwa da kuma maganin cutar kanjamau da tarin fuka kyauta, inda ta bayyana muhimmiyar rawar da suke takawa wajen hada kan jama’a.

 

Da yake mayar da jawabi, Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Taraba kuma Aku Uka na Wukari, HRM Manu Ishaku Adda Ali, ya bayyana ziyarar Misis Tinubu a matsayin alheri ga jihar.

 

Sai dai Sanata Oluremi Tinubu, jim kadan bayan ganawarta da shugabannin gargajiya, ta zarce zuwa filin wasa na Jolly Nyame, inda ta kaddamar da rabon kayayyakin sana’o’in ga ungozoma a fadin yankin Arewa maso Gabas.

 

A nata jawabin, ta kuma jaddada kudirin gwamnatin tarayya na samar da ayyukan kiwon lafiya da nufin rage mace-macen mata da kananan yara a fadin kasar nan.

 

A nasa jawabin, Ministan Lafiya, Farfesa Ali Pate, ya ce a yankin Arewa maso Gabas kadai, an horar da ma’aikatan kiwon lafiya 8,500, daga cikinsu 1,300 daga jihar Taraba.

 

A cewarsa, sama da cibiyoyin kiwon lafiya 1,000 ne ke samun tallafi a duk shekara daga asusun samar da kiwon lafiyai, ciki har da 170 a jihar.

 

Gwamna Agbu Kefas ya yabawa uwargidan shugaban kasar bisa wannan karimcin, inda ya ce jihar ta yi tarayya cikin hangen nesa na shirin sabunta fata.

 

A nata bangaren, uwargidan gwamnan, Misis Agyin Kefas, ita ma ta nuna jin dadin ta bisa yadda aka yi musu dauki, sannan ta yabawa ministan lafiya da walwalar jama’a bisa jajircewar sa.

 

A halin da ake ciki, Sanata Oluremi Tinubu ya mika kayan sana’o’in hannu guda 10,000 ga ungozoma a fadin jihohin Arewa maso Gabas shida, sannan ta mika chekin kudi naira miliyan 50 domin tallafa wa mata 1,000 a jihar Taraba.

 

 

Sani Sulaiman

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taraba uwargidan shugaban jihar Taraba kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

A wannan lokaci da wasu sassa ke kafa shingaye, GCI na gina gadoji. Manufar na kuma karfafa gwiwar tattaunawa, da gudanar da shawarwari tsakanin sassan duniya masu bambance-bambance, ta yadda za a kafa managarcin tsarin hadin kan bil’adama mai dorewa. GCI da ranar tattaunawa tsakanin wayewar kan kasa da kasa ta MDD, za su kara zamewa duniya muhimman manufofi na “tafiya tare a tsira tare”!(Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas