Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Published: 11th, April 2025 GMT
Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da dokar albashi na naira 70,000 a ranar 29 ga watan Yuli na 2024, bayan shafe watanni ana muhawara da kungiyoyin kwadago.
Sabon mafi karancin albashin na wata-wata ya karu da kaso 133 daga naira 30,000 zuwa naira 70,000, sakamakon matsin tattalin arziki da ake fama da shi a kasar nan.
Da yake ba da bayani kan halin da ake ciki, shugaban kungiyar NULGE ya ce, “A zahirin gaskiya muna fuskantar matsaloli da jihohi da dama, kusan jihohi 20 ba su fara aiwatar da mafi karancin albashi ba.
“Muna da Jihohi irinsu Sakkwato, Yobe, Gombe, Zamfara, Kaduna, Imo, Ebonyi, Borno, Kurus Ribas, Abuja, da dai sauransu, wasu sun fara biyan ma’aikatan jiharsu albashi sun bar ma’aikatan kananan hukumomi da malaman firamare, amma mun ci gaba da hada kai da rokon su da su yi wa wadannan ma’aikata abun da ya kamata.
“Wasu daga cikinsu sun yi alkawari amma sun kasa cikawa. Muna fatan nan ba da jimawa ba za a warware wadannan damuwowin,” in ji shi.
Dangane da aiwatar da dokar cin kashin kan kananan hukumomi kuwa, shugaban NULGE ya yi bayanin cewa har zuwa yanzu Babban Bankin Nijeriya bai tuntubi kananan hukumomi kan bude asusun bankuna ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Gwamnoni Mafi Karancin Albashi
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
Daga Bello Wakili
Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da Shugaban Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) da kwamishinoni biyu na hukumar, tare da sabbin manyan sakatarori guda biyar da aka nada a gwamnatin tarayya.
Daga nan ya jagoranci taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Bayan karanta takardar tarihin rayuwarsu, manyan sakatarorin biyar Abdulkarim Ibrahim, Dr John Ezeamama, Dr Abdul-Sule Garba, Dr Isiaku Mohammed da Dr Ukaire Chigbowu, sun dauki rantsuwar kama aiki, sannan suka sanya hannu a kundin rantsuwa.
An kuma rantsar da Dr Aminu Yusuf, wanda shugaban kasa ya nada a matsayin Shugaban NPC a ranar 9 ga Oktoba, da kwamishinoni biyu ciki har da Dr Tonga Betara daga Jihar.
NPC ita ce hukuma da ke da alhakin gudanar da kidayar jama’a a hukumance, yin rajistar haihuwa da mace-mace, da tattara bayanan kimiyyar jama’a domin tsare-tsare.
Majalisar ta yi shiru na minti guda domin tunawa da tsohuwar Ministar Harkokin Waje, Ambasada Joy Ogwu, wadda ta rasu a ranar Litinin, 13 ga watan Oktoban 2025 tana da shekaru 79.