Aminiya:
2025-12-03@15:06:31 GMT

’Yan bindiga sun kashe masunta 3 a Sakkwato

Published: 9th, April 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake zargin mayaƙan Lakurawa ne sun kashe masunta uku a wani hari da suka kai ƙauyen Sanyinna da ke Ƙaramar Hukumar Tangaza a Jihar Sakkwato.

Wata majiyar a ƙauyen ta ce ’yan bindigar sun kashe mutanen ne a lokacin da suka kawo hari da safiyar Talata yayin da mutanen suka fita sana’arsu ta su.

Kazalika, majiyar ta ce ko a ranar Litinin da ta gabata ’yan bindigar sun kai hari garin Sutti da Takkau duk a karamar hukumar inda sun jikkata mutum biyu.

Mataimaki na musamman ga shugaban Ƙaramar Hukumar Tangaza kan tsaro, Alhaji Gazali Raka ya tabbatar da faruwar lamarin.

Alhaji Raka ya bayyana cewa ’yan bindigar sun sace dabbobi da suka haɗa da Shanu da Rakuma da Tumaki da Awaki.

Hadimin shugaban karamar hukumar ya jinjina wa jami’an tsaro kan gaggauta ɗaukar matakin da suka yi na fatattakar ’yan bindigar tare da ƙwato dabbobi da suka yi awon gaba da su.

Aminiya ta ruwaito cewa mutum biyu da suka samu raunin harbin bindiga suna karɓar magani a babban asibitin Tangaza.

Raka ya bayyana damuwarsa kan yadda hare-haren ’yan bindiga ke ƙaruwa a garuruwansu musamman da tsakar rana.

Ya yi kira ga mahukunta da su ƙara ƙaimi don ganin an dawo da zaman lafiya a yankin don samar da ci gaba mai ɗorewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lakurawa Sakkwato yan bindigar yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina

Wata gobara da ta tashi da safiyar Litinin ta kashe magidanci da matarsa da ’ya’yansa uku a unguwar Kofar Sauri da ke cikin garin Katsina.

Wadanda gobarar ta rutsa da su sun haɗa da Muhammad Habibu mai shekara 35, matarsa Fatima Muhammad, da ’ya’yansu uku; Khadija, Abubakar, da Aliyu, wadanda dukkansu suka ƙone har lahira.

Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro

Gobarar ta kuma lalata dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

An gano cewa Muhammad Habibu ma’aikaci ne na wucin gadi a hukumar ruwa ta jihar Katsina kafin rasuwarsa.

Kodayake ba a tabbatar da ainihin dalilin gobarar ba tukuna, mazauna yankin suna zargin ta faru ne sakamakon tashin wuta mai ƙarfi lokacin da aka dawo da lantarki a yankin.

An ce gobarar ta fara ne daga falon gidan sannan ta bazu cikin sauri zuwa sauran sassan gidan, yayin da iyalin ke tsaka da sharer barci.

Bayanai sun ce lokacin da suka fahimci hatsarin, wutar ta riga ta toshe dukkan hanyoyin fita.

Ɗan uwa ga waɗanda suka rasu, Kasim Aliyu, ya ce da misalin ƙarfe 3:00 na safe ya ji muryar wata mace daga nesa tana karanta kalmar shahada: “Innalillahi wa inna ilayhi raji’un.” Da farko ya ɗauka al’ada ce, sai da misalin ƙarfe 3:30 na safe ya fara jin akwai matsala.

Kasim ya ƙara da cewa: “Mai gidan ƙanina ne ubanmu ɗaya. Gobarar ta kama gidan da misalin ƙarfe 3:00 na safe. Na ji wani abu a lokacin amma ban gane ba sai da aka kira ni da misalin ƙarfe 4:00 na safe aka shaida min cewa ƙanina da iyalinsa gaba ɗaya sun mutu a gobarar. Allah ya jikan su.”

Shaidun gani da ido sun ce ƙoƙarin makwabta da masu taimakon gaggawa wajen kashe gobarar ya ci tura.

Sun yi korafin cewa jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Katsina sun iso daga baya amma zuwan nasu bai yi wani tasiri ba sosai.

Wani mazaunin yankin, Musa Hamza, ya ce: “Ina ganin lokacin da hukumar kashe gobara ta iso, mutanen cikin gidan sun riga sun mutu a gobarar. Amma zan iya cewa sun yi iya ƙoƙarinsu wajen kashe wutar, sai dai ba su samu nasarar ceto iyalin ba. Allah ya jikan su.”

Wani makwabci, Magaji Bala, ya yi korafi cewa mazauna yankin sau da yawa suna shafe kwanaki ba tare da lantarki ba, sai kuma tashin wuta mai ƙarfi ya jawo barna duk lokacin da aka dawo da wuta.

“Irin wannan lamari ya taɓa faruwa a wasu sassan garin Katsina. Kwanan nan ma kusan irin haka ya faru. Wannan ya sa dole mutane su yi taka-tsantsan,” in ji shi.

Da aka tuntubi Babban Jami’in Kashe Gobara na jihar Katsina, Rabe Audi Kurmuyal, ya tabbatar da cewa ma’aikatansa sun kashe gobarar, sabanin ikirarin da ake yi cewa sun iso daga baya.

Wasu mazauna sun dora laifin kan matsalar sauyin wuta da ake yawan samu daga kamfanin rarraba na shiyyar Kano (KEDCO), suna cewa yawan katsewa da dawowa da ƙarfin lantarki mai yawa na lalata kayan lantarki.

Sai dai kamfanin ya musanta zargin, inda ya ca ba zai yiwu a ce laifinsu ba ne, kasancewar gidan shi kadai ya kone a unguwar mai gidaje sama da 5,000.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 12 da ɓacewarsu a Borno
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • ’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato