’Yan bindiga sun kashe masunta 3 a Sakkwato
Published: 9th, April 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake zargin mayaƙan Lakurawa ne sun kashe masunta uku a wani hari da suka kai ƙauyen Sanyinna da ke Ƙaramar Hukumar Tangaza a Jihar Sakkwato.
Wata majiyar a ƙauyen ta ce ’yan bindigar sun kashe mutanen ne a lokacin da suka kawo hari da safiyar Talata yayin da mutanen suka fita sana’arsu ta su.
Kazalika, majiyar ta ce ko a ranar Litinin da ta gabata ’yan bindigar sun kai hari garin Sutti da Takkau duk a karamar hukumar inda sun jikkata mutum biyu.
Mataimaki na musamman ga shugaban Ƙaramar Hukumar Tangaza kan tsaro, Alhaji Gazali Raka ya tabbatar da faruwar lamarin.
Alhaji Raka ya bayyana cewa ’yan bindigar sun sace dabbobi da suka haɗa da Shanu da Rakuma da Tumaki da Awaki.
Hadimin shugaban karamar hukumar ya jinjina wa jami’an tsaro kan gaggauta ɗaukar matakin da suka yi na fatattakar ’yan bindigar tare da ƙwato dabbobi da suka yi awon gaba da su.
Aminiya ta ruwaito cewa mutum biyu da suka samu raunin harbin bindiga suna karɓar magani a babban asibitin Tangaza.
Raka ya bayyana damuwarsa kan yadda hare-haren ’yan bindiga ke ƙaruwa a garuruwansu musamman da tsakar rana.
Ya yi kira ga mahukunta da su ƙara ƙaimi don ganin an dawo da zaman lafiya a yankin don samar da ci gaba mai ɗorewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Lakurawa Sakkwato yan bindigar yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
Wata rundunar haɗin gwiwa ta jami’an tsaro ta samu nasarar kuɓutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su da shanu da aka sace a Jihar Kebbi.
Bayanai sun ce an sace mutanen da dabbobin ne a ƙauyukan Ukuhu da Kokanawa a Karamar Hukumar Danko Wasagu ta jihar.
‘ADC za ta mayar da APC jam’iyyar adawa a 2027’ Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADCWani daraktan tsaro a Gwamnatin Kebbi, Abdurrahama Zagga ne ya sanar wa manema labarai nasarar da aka samu a ranar Talata, inda ya ce an kai samamen ne bayan umarni da aka samu daga Gwamna Nasiru Idris bisa bayanan sirri da aka tattaro a yankin.
A cewar Zagga, tawagar jami’an tsaro ta fatattaki ’yan ta’addan da suka yi garkuwa da mutanen da kuma shanun da suka sace a wani gulbi da ke iyaka da Jihar Zamfara.
“Mutane da aka ceto an mika su ga iyalansu. Kuma wannan abin farin ciki ne ga gwamna musamman a kokarin da jami’an tsaro suke yi, lamarin da zai kara inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin masarautar Zuru.”
Ya bayyana fatan da suke da shi na kawar da ɓarayin shanu da ’yan bindigar Lukurawa a yankin Zuru da Argungu.