Aminiya:
2025-06-15@09:39:23 GMT

Arsenal ta gasa wa Madrid aya a hannu

Published: 9th, April 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta lallasa Real Madrid a daren nan a karawar da suka yi ta kwata-fainal a Gasar Zakarun Turai.

Arsenal dai ta doke Real Madrid da ci 3-0 a fafatawar da suka yi a filin wasa na Emirates da ke Landan.

Boko Haram na sake ƙwace ikon wasu yankuna a Borno — Zulum Kisan Isuhu Yellow: ’Yan bindiga sun kai harin ɗaukar fansa

An kammala minti 45 na karawar babu ci, sai dai alƙaluma sun nuna Arsenal ta kai farmaki sau huɗu yayin da Real ta kai hari sau biyar.

Duk da cewa babu ɓangaren da ya samu nasarar zura ƙwallo amma wasan wanda Irfan Peljto na ƙasar Bosnia Herzegovina ya yi alƙalanci ya yi matuƙar zafi tsakanin ɓangarorin biyu.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne ɗan wasan tsakiya na Arsenal, Declan Rice ne ya zura ƙwallon farko a minti na 58 ta hanyar bugun tazara bayan da ’yan wasan Madrid suka yi wa Bukayo Saka ƙeta.

A minti na 70 ne Declan Rice ya ƙara zura ƙwallo ta biyu a ragar Real Madrid ta hanyar bugun tazara kamar yadda ya yi a karon farko.

A yayin da aka ci gaba da ɗauki ba daɗi ne Mikel Merino ya zura ƙwallo ta uku a minti na 75 da take wasa, bayan ɗan wasa Lewis Skelly ya zuro masa ƙwallon daga gefe.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arsenal

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu

Hukumomin ’yan sandan Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu hukumomin tsaro sun samu gagarumar nasara a ƙoƙarin da suke na daƙile munanan laifuka a ƙasar.

Na baya-bayan nan dai shi ne ceto mutanen da aka sace, da kashe wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma ƙwato manyan bindigogi da alburusai a jihohin Delta da Katsina.

Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce a jihar Katsina an samu gagarumar nasara a ranar 8 ga watan Yunin 2025, inda haɗin gwiwar JTF da suka haɗa da jami’an ’yan sanda da sauran jami’an tsaro suka daƙile wani yunƙurin yin garkuwa da mutane a hanyar ƙauyen Danmusa  zuwa  Mara Dangeza a ƙaramar hukumar Danmusa.

Adejobi ya ce hakan na iya yiwuwa ne ta hanyar shigar da wasu gungun ’yan bindiga da suka yi yunƙurin guduwa da waɗanda aka yi garkuwa da su a wani artabu da ya kai ga ceto mutum 11.

Nasarar da aka samu yankin Kudu maso Kudu

A halin da ake ciki kuma, a yankin Kudu maso Kudu, Jihar Delta, hukumar ’yan sanda ta kama wani Abubakar Hassan, wanda babban wanda ake zargi da aikata laifin satar mutane ne a tsakanin jihohin Delta da Ribas da Imo, da Enugu.

Jami’an da ke da alaƙa da samun nasarar sun yi hakan ne yayin da suke aiki da sahihan bayanai.

A yayin da ake yi masa tambayoyi, Hassan ya bayyana cewa shi ne ya jagoranci gudanar da hari a yankin Ughelli-Ozoro na jihar mai arzikin man fetur.

Ya kuma jagoranci jami’an ’yan sanda zuwa maɓoyarsa a wani daji da ke Ozoro. A can jami’an sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da tarin alburusai huɗu da harsashi guda talatin da biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
  • Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa