Aminiya:
2025-10-14@00:31:35 GMT

Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi

Published: 24th, February 2025 GMT

Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan, Sheikh Ahmad Gumi, ya ce har yanzu Najeriya na neman shugabanni nagari da za su fifita jin daɗin al’umma maimakon mayar da hankali kan wajen tara wa kansu dukiya.

Ya bayyana hakan ne yayin bikin karramawa da ƙungiyar tsofaffin ɗaliban Makarantar Firamare ta Sultan Bello (SUBOPA), ta shirya domin girmama wasu mambobinta biyu – Manjo Janar Abdulmalik Jibrin (mai ritaya) da Birgediya Janar Abdulkadir Gumi (mai ritaya), bisa sababbin muƙaman da suka samu a gwamnati.

Arewa na buƙatar haɗa kai da Kudu Maso Kudu don ceto Najeriya — El-Rufai Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP

An naɗa Manjo Janar Jibrin a matsayin Sakatare na Hukumar Kula da Tsaro na Fararen Hula, yayin da aka naɗa Birgediya Janar Gumi a matsayin Shugaban Kwamitin Tallafin Tsaro na Jihar Zamfara.

Sheikh Gumi ya yaba wa Manjo Janar Jibrin bisa aiki tuƙuru da ɗa’a, inda ya ce har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni kamar shi waɗanda ke da gaskiya, horo mai kyau, da kuma kishin al’umma.

“Wannan ya faru ne saboda Najeriya na matuƙar buƙatar shugabanni nagari da za su jagoranci ƙasar nan.

“Muna buƙatar mutane masu tarbiyya da ladabi waɗanda ke da niyyar taimaka wa wasu, ba kawai kansu ba.

“Mutanen da ke da kyawawan halaye da ɗabi’u su ne ya kamata ake bai wa muƙaman shugabanci a ƙasar nan,” in ji shi.

Ya kuma soki shugabannin yanzu, inda ya ce: “Ba irin shugabannin da muke da yanzu a ƙasar nan ba, waɗanda kawai ke tunanin kansu da iyalansu.”

Da yake magana kan matsalolin da Najeriya ke fuskanta, Sheikh Gumi ya nuna damuwarsa kan tasirin matsalar tsaro, musamman a jihohin da suka haɗa da Zamfara, inda matsalar ta janyo koma baya a ɓangaren ilimi tare da haifar da rashin zaman lafiya a wasu yankuna.

Ya jinjina wa Gwamnatin Jihar Zamfara bisa bai wa Birgediya Janar Gumi muƙami, wanda ya ce zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro.

A nasa jawabin, Shugaban SUBOPA, Mohammad Babayo Hassan, ya ce naɗin da aka yi wa mambobinsu ba kawai nasararsu ba ce, wata alama ce ta ɗabi’u da ƙwazon da suka koya daga makarantarsu.

Da yake magana a madadin waɗanda aka karrama, Manjo Janar Abdulmalik Jibrin ya keɓe lambar yabon ba ta shi ce shi kaɗai ba, face ta dukkan mambobin ƙungiyar ne.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Najeriya na Manjo Janar na buƙatar

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ba Zata Halarci Zaman Taron Sharm El-Sheikh Ba Saboda Wasu Dalilai Da Ta Byyana

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana dalilin da ya sa Iran ba za ta halarci taron na Sharm el-Sheikh ba

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana dangane da rashin halartar jamhuriyar Musulunci ta Iran zuwa taron na Sharm el-Sheikh cewa, ba za su iya tunkarar wadanda suka kaddamar da hare-haren wuce gona da iri kan al’ummar Iran da kuma ci gaba da yi musu barazana da kuma sanya musu takunkumi ba.

Araqchi ya rubuta a shafinsa na yanar gizo a dandalin X da sanyin safiyar yau litinin cewa: “Iran ta nuna matukar jin dadin ta ga gayyatar da shugaba Sisi ya yi wa Iran na halartar taron na Sharm el-Sheikh. Duk da Muradin Iran din na tattaunawa ta diflomasiyya, Araqchi ya ce shi ko shugaba Pezeshkian ba za su iya tunkarar wadanda suka kai wa al’ummar Iran hari da kuma ci gaba da yi mata barazana da kuma sanya mata takunkumi.”

Ya kara da cewa: Duk da haka, Iran tana maraba da duk wani shiri da zai kawo karshen kisan kiyashin da gwamnatin mamayar Isra’ila ke yi a Gaza da kuma bukatar kai wa ga janye sojojin mamaya daga yankin.

Araqchi ya jaddada cewa: Falasdinawa suna da ‘yancin fahimtar ainihin hakkinsu na cin gashin kansu, kuma dukkan kasashe, fiye da kowane lokaci, suna da alhakin taimaka musu tare da goyon bayan wannan bukata ta doka da ta dace.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gayyaci Mukaddashin Jakadan Kasar Oman Zuwa Ma’aikatar Harkokin Wajenta October 13, 2025 Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta October 13, 2025 Cibiyar Lafiya Ta Nasser Ta Ce: Yaran Gaza 5,500 Suna Bukatar Agajin Gaggawa A Kasashen Waje October 13, 2025 Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk October 13, 2025 Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza October 12, 2025 ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar October 12, 2025 Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice   October 12, 2025 Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine October 12, 2025 Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Amurka Donal Trump Ya Isa HKI Kafin Taron Sharm Sheikh
  • Iran Ba Zata Halarci Zaman Taron Sharm El-Sheikh Ba Saboda Wasu Dalilai Da Ta Byyana
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Yanzu-Yanzu: ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki Na Tsawon Mako Biyu
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa