Aminiya:
2025-08-13@08:50:14 GMT

Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi

Published: 24th, February 2025 GMT

Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan, Sheikh Ahmad Gumi, ya ce har yanzu Najeriya na neman shugabanni nagari da za su fifita jin daɗin al’umma maimakon mayar da hankali kan wajen tara wa kansu dukiya.

Ya bayyana hakan ne yayin bikin karramawa da ƙungiyar tsofaffin ɗaliban Makarantar Firamare ta Sultan Bello (SUBOPA), ta shirya domin girmama wasu mambobinta biyu – Manjo Janar Abdulmalik Jibrin (mai ritaya) da Birgediya Janar Abdulkadir Gumi (mai ritaya), bisa sababbin muƙaman da suka samu a gwamnati.

Arewa na buƙatar haɗa kai da Kudu Maso Kudu don ceto Najeriya — El-Rufai Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP

An naɗa Manjo Janar Jibrin a matsayin Sakatare na Hukumar Kula da Tsaro na Fararen Hula, yayin da aka naɗa Birgediya Janar Gumi a matsayin Shugaban Kwamitin Tallafin Tsaro na Jihar Zamfara.

Sheikh Gumi ya yaba wa Manjo Janar Jibrin bisa aiki tuƙuru da ɗa’a, inda ya ce har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni kamar shi waɗanda ke da gaskiya, horo mai kyau, da kuma kishin al’umma.

“Wannan ya faru ne saboda Najeriya na matuƙar buƙatar shugabanni nagari da za su jagoranci ƙasar nan.

“Muna buƙatar mutane masu tarbiyya da ladabi waɗanda ke da niyyar taimaka wa wasu, ba kawai kansu ba.

“Mutanen da ke da kyawawan halaye da ɗabi’u su ne ya kamata ake bai wa muƙaman shugabanci a ƙasar nan,” in ji shi.

Ya kuma soki shugabannin yanzu, inda ya ce: “Ba irin shugabannin da muke da yanzu a ƙasar nan ba, waɗanda kawai ke tunanin kansu da iyalansu.”

Da yake magana kan matsalolin da Najeriya ke fuskanta, Sheikh Gumi ya nuna damuwarsa kan tasirin matsalar tsaro, musamman a jihohin da suka haɗa da Zamfara, inda matsalar ta janyo koma baya a ɓangaren ilimi tare da haifar da rashin zaman lafiya a wasu yankuna.

Ya jinjina wa Gwamnatin Jihar Zamfara bisa bai wa Birgediya Janar Gumi muƙami, wanda ya ce zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro.

A nasa jawabin, Shugaban SUBOPA, Mohammad Babayo Hassan, ya ce naɗin da aka yi wa mambobinsu ba kawai nasararsu ba ce, wata alama ce ta ɗabi’u da ƙwazon da suka koya daga makarantarsu.

Da yake magana a madadin waɗanda aka karrama, Manjo Janar Abdulmalik Jibrin ya keɓe lambar yabon ba ta shi ce shi kaɗai ba, face ta dukkan mambobin ƙungiyar ne.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Najeriya na Manjo Janar na buƙatar

এছাড়াও পড়ুন:

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

“Na taɓa zama abar kwatance, musamman a ɓangaren da shafi kuɗi, suna, girmamawa, amma kuskuren da na yi ya zama dalilin da yasa masana’antar ta juya min baya, sakamakon babu abin da na iya ko na sani face; harkar ta fim. Halin da ake ciki yanzu, babu wani tallafi, babu aikin yi, akwai lokacin da ina da ɗimbin masoya da suke son aurena da kuma nuna min soyayya, amma sai na kasa zaɓen wanda zan ci gaba da rayuwata da shi a wancan lokaci.

Babban dalilin da ya jawo min koma-baya a harkar fim shi ne, hatsarin da na samu na mota, wanda Allah ya jarrabce ni da shi, na yi hatsarin mota da har sai da na samu karaya huɗu a ƙafata, sannan kuma na samu buguwa a kaina da har sai da na manta da komai na rayuwa da na sani a wancan lokaci, bugu da gari; fuskata ta samu raunuka masu yawa da suka canza mani fasalin fuskar tawa, hakan ya sa na ɗauki tsawon lokaci ina jinya.

Da ta ke amsa tambaya a kan ko ‘yan’uwan sana’arta na Kannywood sun taimaka mata a lokacin da take cikin wannan mawuyacin hali? Ummi ta ce, duk da babu wani wanda ya ɗauki nauyin jinyarta a wancan lokaci, amma dai ba za ta taɓa mantawa da yadda suka riƙa zuwa har gida suna gaishe ta ba, “Ni na ɗauki nauyin jinyar kaina, saboda bakin gwargwado ina da abin da zan iya ɗaukar nauyin jinyata”, in ji Ummi.

Dangane da da-na-sanin da ta ke yi a rayuwa kuma, Ummi ta ce; babu wani abu da take da-na-sanin rashin yi da ya wuce aure, domin da a ce ta yi aure, zuwa yanzu wataƙila da Allah ya azurta ta da samun zuri’a, waɗanda za su riƙa kula da ita yanzu da kuma bayan ta tsufa. “Don haka, ina fatan yin aure kafin rayuwata ta zo ƙarshe”.

Daga ƙarshe, tsohuwar jarumar ta buƙaci matasa masu tasowa a masana’antar Kannywood, da kada su maimaita irin kuskuren da da yawa daga cikin tsoffin jarumai mata suka yi, “Ina shawartar duka wata mace mai lokaci a masana’antar Kannywood yanzu, da ta tabbatar da cewa; ta saka hannun jari a wasu wuraren kasuwanci da za su riƙa samar mata da wani abu ta yadda ko da lokacin ɗaukakarta ya wuce, za ta ci gaba da yi; domin kula da rayuwarta.

Dalili kuwa shi ne, duk irin ɗaukakar da kika samu a yanzu, lokaci na nan zuwa da dole zai gushe, ki zama kamar ba ki taɓa samun wannan ɗaukaka ba, kamar yadda yanzu ake yi babu mu, duk kuwa da irin shaharar da muka samu a lokutan baya.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Janar Hatami ya karbi bakuncin babban hafsan hafsoshin sojin Afirka ta kudu
  • ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC
  • NAJERIYA A YAU: Yadda matasa ke bayar da gudunmawa ga ci-gaban al’umma
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Damina Ke Shafar Masu Ƙananan Sana’o’i
  • Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali
  • UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa