Limamin Juma’ar Birnin Tehran Ya Ce; Al’ummar Iran Sun Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka
Published: 14th, February 2025 GMT
Limamin da ya jagoranci sallar Jumu’a a birnin Tehran ya bayyana cewa: Al’ummar Iran sun mayar da martani ga shugaban Amurka ta hanyar gudanar da bikin tunawa da samun nasarar juyin juya halin Musulunci
Limamin da ya jagoranci sallar Juma’a a birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya bayyana cewa: Al’ummar Iran sun mayar da martani da kakkausar murya ga kalamai da kuma matakin da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dauka ta hanyar halartar gagarumar zanga-zangar tunawa da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a kasar Iran.
Ayatullah Khatami ya kara da cewa: A yau daga mimbarin Juma’a da ke birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran yana tabbatar da cewa: Miliyoyin Iraniyawa ne suka halarci wannan zanga-zangar tare da jaddada sha’awa, kuma irin wannan zanga-zanga ta bana ta fi ta kowace shekara daraja. Limamin Juma’ar ya jaddada cewa: Makiya suna magana ne a kan wuce gona da iri da bama-bamai, don haka ya ce: Trump mahaukaci ne wanda yake dauke da nazarin cewa; Ku gabatar da mu ta hanyar da za su tsorata; Ya kara da cewa: Ku gaya wa mutane cewa yatsarmu tana kan hanya, kuma idan kun yi rashin biyayya, za mu kai muku hari, Sayyid Khatami ya kara da cewa: Hakika al’ummar Iran suna daukar Trump a matsayin mahaukaci ne, kuma zasu kara masa hauka da yardan Allah Madaukaki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas aragchi da tokwransa na kasar Masar Badr Abdullati da kuma tokwaransu na kasar Omman Badr ben Hamad Al-Busaidi sun tattauna a tsakaninsu a birnin Oslo inda suka halattar taron tattaunawa ta 22th da ake gudanarwa a birnin na Oslo babban birnin kasar Norway.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa bangarorin biyu sun yi maganar rikice-rikicen da ke faruwa a yankin da kuma hanyar warwaresu.
Taron oslo na shekara shekara dai a wannan karon ya maida hankali ne kan abubuwan da suke faruwa a yankin Asiya da kuma hanyoyin da yakamata abi don rage halin da ake ciki a yankin. Musamman matsalar yaki da kima kissan kiyashin da ke faruwa a Gaza da kuma yadda HKI ta sabawa dukkan dokokin kasa da kasa a yakin.
Jaridar The National ta kasar Amurka ta bada labarin cewa kasashen Iran da masar wadanda basa da dangantakar Diblomasiyya na kimani shekar 40 sun tattauna batun maida huldar jakadanci a tsakaninsu, inda daga cikin ministan harkokin wajen Masar ya bukaci a shafin hoton Khalid Islam buli wanda ya kashe tsohon shugabann kasar Masar a shekara 1980 wanda aka sanya a kan wani babban titi a birnin Tehran. Har yanzun dai ba’aji ta bakin gwamnatinn kasar Iran kan hakan ba.