Limamin Juma’ar Birnin Tehran Ya Ce; Al’ummar Iran Sun Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka
Published: 14th, February 2025 GMT
Limamin da ya jagoranci sallar Jumu’a a birnin Tehran ya bayyana cewa: Al’ummar Iran sun mayar da martani ga shugaban Amurka ta hanyar gudanar da bikin tunawa da samun nasarar juyin juya halin Musulunci
Limamin da ya jagoranci sallar Juma’a a birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami ya bayyana cewa: Al’ummar Iran sun mayar da martani da kakkausar murya ga kalamai da kuma matakin da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dauka ta hanyar halartar gagarumar zanga-zangar tunawa da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a kasar Iran.
Ayatullah Khatami ya kara da cewa: A yau daga mimbarin Juma’a da ke birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran yana tabbatar da cewa: Miliyoyin Iraniyawa ne suka halarci wannan zanga-zangar tare da jaddada sha’awa, kuma irin wannan zanga-zanga ta bana ta fi ta kowace shekara daraja. Limamin Juma’ar ya jaddada cewa: Makiya suna magana ne a kan wuce gona da iri da bama-bamai, don haka ya ce: Trump mahaukaci ne wanda yake dauke da nazarin cewa; Ku gabatar da mu ta hanyar da za su tsorata; Ya kara da cewa: Ku gaya wa mutane cewa yatsarmu tana kan hanya, kuma idan kun yi rashin biyayya, za mu kai muku hari, Sayyid Khatami ya kara da cewa: Hakika al’ummar Iran suna daukar Trump a matsayin mahaukaci ne, kuma zasu kara masa hauka da yardan Allah Madaukaki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
Babban hafsan hafsoshin sojan Iran Manjo janar Musawi ya ce, ko kadan Iran ba ta yarda ko gaskata alkawullan Amurka,balle kuma zancen ‘yan sahayoniya.
Babban hafsan hafsoshin sojan na Iran ya kuma kara da cewa, sojojin kasar suna cikin Shirin ko-ta-kwana domin kalubalantar duk wan igigi na abokan gaba.
Manjo janar Musawi ya bayyana hakan ne dai a lokacin da ya yi tattaunawa ta wayar tarho da ministan tsaron kasar Tajikistan Manjo janar Imam Ali Sabir Zadeh.
A nashi gefen, ministan tsaron kasar ta Tajikistan, ya fara da yi wa janar Musawi murnar zabarsa sabon hafsan hafsoshin sojan kasar ta Iran, sannan kuma ya nuna bakin cikinsa akan rashin kwamandojin sojan Iran da su ka yi shahada a sanadiyyar harin ta’addancin HKI.
Manjo janar Imam Ali Sabir Zadeh ya kuma kara da cewa, al’ummar kasar Tajikinstan sun yi bakin ciki, don haka suna isar da ta’aziyyarsu ga al’ummar Iran.
Har ila yau minstan tsaron kasar ta Tajikistan ya yi ishara da tarayya akan harshe da al’ada da kasashen biyu su ka yi, haka nan kuma tarihi.
Haka nan kuma manjo janar Musawi ya yi wa Tajikistan godiya akan yadda ta kasance a tare da Iran a lokacin yakin kwanaki 12, lamarin da ya kara karfin alakar kasashen biyu.