Leadership News Hausa:
2025-06-15@13:47:52 GMT

Hakuri Da Baiwa (Kyautar) Manzon Allah (SAW)

Published: 14th, February 2025 GMT

Hakuri Da Baiwa (Kyautar) Manzon Allah (SAW)

Annabi (SAW) a cikin dukkan kyawawan halaye ba a kamanta shi da kowa.

Jabir dan Abdullahi (RA) yana cewa, ba a tava tambayar Annabi (SAW) da wani abu ba ya ce babu.

Abdullahi dan Abbas (RA) yana cewa “Annabi (SAW) ya kasance mafi baiwar Mutane da alkairi, lokacin da Annabi ya fi baiwa, shi ne lokacin watan Azumin Ramadana, ya kasance idan ya hadu da Mala’ika Jibrilu, Mala’ika Jibrilu yana zuwa suna Musaffan Karatun Alkur’ani da Annabi (SAW) duk watan Ramadana sau daya, sai shekarar wafati ce suka yi sau biyu.

Shi ya sa, duk musulmai suna da baiwa da kyauta amma in watan Ramadana ya zo sai ka ga sun kara ninkawa.

An karvo hadisi daga Anas khadimin Manzon Allah (SAW) ya ce, wani Mutum ya nemi kyauta daga Manzon Alla (SAW), sai ya ba shi Tumaki tsakanin duwatsu biyu cike da dabbobi amma Annabi sai da ya ba shi dukkansu (SAW). Wanann ya faru ne a lokacin yakin Hunaini, Sahabin shi ne Safwan bin Umayya. Annabi ya gan shi yana ta kallon tumakin, sai ya tambaye shi, sun burge ka ne? sai ya ce Ya Rasulallahi wane Balarabe ne zai ce bai son wannan, take Annabi ya ce masa ya dau sanda ya kora su ya bar masa. Sai Safwan ya koma wurin mutanensa ya ce musu ku Musulunta sabida ‘Muhammad’ (SAW) yana bayar da kyauta irin wacce ba ya tsoron talauci.

 

Wata rana Manzon Allah (SAW) ya bai wa Abu Sufyan Rakumi 100 a lokaci daya, ya bayar da dukiya mai yawa da ba a san adadinta ba da aka samo ganima a yakin Hunaini.

Yakin Hunaini, yaki ne da ya kasance bayan fitowar Annabi (SAW) da rundunar yaki sama da 10,000 don bude Makkah, amma kuma sarkin Hunain ya karya alkawari da Annabi (SAW), ya ji labarin rundunar da Annabi (SAW) ya fito da ita, sai ya tara ninkin ta Annabi Uku (30,000) kuma ya ce kowannensu ya fito da duk dukiyar da ya mallaka da kuma iyalansa (Mata da Yara), rundunar Hunaini dukkansu maharba ne. Bayan Annabi (SAW) ya bude Makkah, ya samu karin mayaka, sai ya nufi Hunaini, wasu daga cikin Sahabbai suka fara alfahari cewa “Yau babu wata runduna da za ta iya kayar da mu”, bayan Annabi ya fada wani kwari a hanyar zuwa Hunaini, ashe duk rundunar maharba su 30,000 suna sama kowanne da kibiya a hannu, kawai sai suka yo ruwan kibiyoyi ga sahabbai, nan fa kowa ya arta a guje sai Mutum 100 kacal, Annabi (SAW) ya watsa musu kasa duk ta cike idanuwan maharban sannan ya sa Baffansa Abbas ya kira Mutanen Madina. Allah ya ba wa Annabi (SAW) da rundunarsa Nasara, Kafirai sun bar dukiyoyinsu da Iyalansu.

 

Wannan dukiya da suka bari mai yawa, Annabi (SAW) ya jira ko za su dawo su Musulunta ya mayar musu da dukiyarsu amma ba su dawo a lokaci ba har sai da Annabi (SAW) ya rabar da dukiyar baki daya sannan suka dawo.

Annabi (SAW) ya nemi zabinsu a kan wanda ya fi, muhimmanci a wurinsu, Dukiyarsu ko Iyalansu, sai suka zavi Iyalansu, an ce Annabi ya maida musu da ‘yan mata sama da 6,000.

Annabi (SAW) ya ba wa baffansa Abbas dukiya (zinare) ya dauka iya karfinshi, an kawo wa Annabi (SAW) daga ganimar yakin kudi Dirhami 90,000, Annabi (SAW) ya sa aka shimfida tabarma a Masallaci, har sai da ya rabar da kudin gaba daya, Abbas ya ce ya dana a yakin Badr sai da kasa na biya fansar Mutum Uku, kai ka maida ni Talaka don haka yanzu ga kudi a maida min da kudina, shi ne Annabi (SAW) ya hore shi da ya diba zinare iya karfinshi. Bayan an gama rabo sai wani ya zo ya ce Ya Rasulallahi ina nawa? Annabi ya ce masa komai ya kare amma ya je ya ci bashi zai biya masa in an samu kudi. Sai Sayyadina Umar ya ce Ya Rasulallahi Allah bai dora maka abin da ba zaka iya ba, Annabi (SAW) ya ki wannan maganar, sai wani daga cikin Sahabbai ya ce Ya Rasulallahi ka ciyar, kar ka ji tsoron wani talauci daga Ubangjin Al’arshi, sai Annabi (SAW) ya yi farin ciki kuma aka ga bishara a fuskarsa.

An karvo daga Mu’awwizu bin Afra’a (Sadaukin Badr) yana cewa, wata rana na zo wurin Annabi (SAW) ina dauke da faifai da Dabino a kai, hakikanin Hadisin ‘yarshi ce ya aiko ba shi ne ya zo da kanshi ba, ta ce na zo wurin Annabi (SAW) da faifai akwai Dabino danye da Vuluvutu danye wanda bai girma sosai ba a kanshi, sai Annabi (SAW) ya ciko hannunsa da kayan kwalliya na Mata (Awarwaro) na zinari ya ba ni.

Khadiminsa Anas, ya kasance yana cewa, Annabi (SAW) ba ya ajiye komai sabida gobe a kan-kansa amma yana ajiye wa Matansa abincin Shekara, don haka in sun ba shi ya gode, in ba su bashi ba, daman nasu ne.

Yana daga cikin kyautar Annabi (SAW), wata rana wani ya tava zuwa wurinsa yana neman taimako Annabi kuma (SAW) lokacin babu, sai ya nemo rancen rabin masaki na Dabino ya bashi. Wanda kuma ya bai wa Annabi (SAW) wannan rancen, da ya zo amsar bashinsa sai (SAW) ya ba shi Masaki cikakke. Annabi ya ce masa, rabin biyan bashi ne, dayan rabin kuma kyauta ce.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ya ce Ya Rasulallahi

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe

An fargabar cewa ’yan bindiga sun kashe akalla mutum 100 a wani hari da suka kai a garin Yelewata da ke yankin Karamar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.

Aminiya ta ruwaito cewa maharan sun far ma al’ummar garin na Yelewata ne a cikin daren ranar Juma’a wayewar garin Asabar.

Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa

Wadanda suka shaida harin na Yelewata sun ce maharan sun mamayi garin ne kafin karfe 12 na dare, inda suka kwashe sama da sa’a biyu suna ta’annati ba tare da wani dauki daga jami’an tsaro ba.

Da yake zantawa da Kamfanin Dillancin Labarai na AFP, wani mai magana da yawun fadar gwamnatin Benuwe, Tersoo Kula, ya tabbatar da faruwar lamarin yana mai cewa maharan sun kone gidaje da dama.

Sai dai ya ce jami’an gwamnati da suka kai ziyara yankin na Yelwata sun samu cewa wadanda aka kashe ba su wuce mutum 45 ba.

Shi ma mai magana da yawun ’yan sandan jihar, Udeme Edet, ya ce jami’ansu sun yi musayar wuta da maharan.

Haka kuma, an wani harin na daban da ya auku an kashe sojoji biyu a garin Daudu, shi ma a yankin karamar hukumar ta Guma.

Wannan harin shi ne na uku a baya-bayan nan a garin Yelewata wanda ke kan iyakar jihar ta Benuwe da Nasarawa a cikin mako daya.

Ana iya tuna cewa a watan da ya gabata ne wasu mahara da ake zargin makiyaya ne suka kashe kimanin mutum 20 a karamar hukumar Gwer ta Yamma a jihar ta Benuwe.

Kungiyar Amnesty mai fafutikar kare hakkin dan Adam ta yi kira ga gwamnatin da ta dauki matakin dakile zubar jini da salwantar rayukan al’umma a kasar.

Amnesty ta ce gazawar gwamnatin Nijeriyar ce ta sanya asarar rayukan al’ummar kasar ta zama ruwan dare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa