De Bruyne zai yi bankwana da Manchester City a ƙarshen kaka
Published: 6th, April 2025 GMT
Ɗan wasan ƙasar Belgium, Kevin De Bruyne, ya sanar da cewa zai yi bankwana da ƙungiyar Manchester City ta Ingila a ƙarshen kakar bana.
Fitaccen ɗan wasan tsakiyar mai shekaru 33 ya sanar da hakan ne cikin wata saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta na X.
Tsohon Gwamnan Oyo Olunloyo ya riga mu gidan gaskiya Finafinan Kannywood da suke tashe da kuma manyan marubutansuDe Bruyne ɗan asalin ƙasar Belgium ya tabbatar da cewa waɗannan su ne watanninsa na ƙarshe a matsayin ɗan wasan Manchester City.
De Bruyne ya je Manchester City a shekarar 2015 daga Wolfsburg, inda ya lashe duka manyan gasar ƙwallon ƙafa tare da ƙungiyar ta City, ciki har da gasar Firimiya ta Ingila da Gasar Zakarun Turai.
Kwantaraginsa a City zai ƙare a ƙarshen Yunin bana, amma har yanzu ba a tabbatar ko zai haska ba a wasannin da City za ta buga daga 14 ga Yuni zuwa 13 ga Yuli.
“Kowane labari yana zuwa ƙarshe, amma lallai wannan ya kasance babi mafi kyau a gare ni.
“Mu mori waɗannan lokutan tare har zuwa ƙarshe,” a cewarsa.
De Bruyne ya buga wasanni 280 a gasar Firimiya, kuma ya ci ƙwallaye 70 da tallafin ƙwallaye 118.
Hakan ya sa shi yake biye da Ryan Giggs tsohon ɗan wasan Manchester United, wanda yake riƙe da kambun wanda ya fi ba da tallafin cin ƙwallo a tarihin Firimiya, da ƙwallaye 162.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
Aƙalla mutum 26 ne suka rasu sakamakon wasu sabbin hare-haren da aka kai wasu ƙauyuka a Jihar Binuwai.
Hare-haren sun faru ne a yankunan Ƙaramar Hukumar Makurdi da Katsina-Ala tsakanin ƙarfe 12 na dare zuwa 2 na daren ranar Alhamis.
Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasuA Ƙaramar Hukumar Makurdi, wasu ’yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Mtswenem da Akondotyough Bawa, inda suka kashe mutum 25.
Haka kuma, an kashe mutum ɗaya a wani hari daban da aka kai ƙauyukan Kenvanger da Agbami a Ƙaramar Hukumar Katsina-Ala.
Wasu mazauna yankin sun ce ’yan bindigar sun shiga gidajen mutane suna harbin su yayin da suke barci, suna amfani da bindigogi da adduna.
Wani wanda ya tsira mai suna Iorpuu, ya ce mata da yara suna cikin waɗanda aka kashe, kuma har yanzu ana neman wasu da suka ɓace.
Ya ƙara da cewa wasu sun mutu ne a kan hanyarsu ta zuwa asibiti.
Wani ganau ya ce an fara kai harin ne wani ƙauye kusa da Jami’ar Noma da Fasaha ta Makurdi, inda aka kashe mutane huɗu.
Daga nan suka wuce wani ƙauye a kusa da unguwar Low Cost suka ci gaba da kashe mutane har adadin gawarwakin ya kai 25.
A Katsina-Ala, ’yan bindigar sun kai hari ƙauyukan Kenvanger da Agbami da misalin ƙarfe 1 na dare.
An ce sun yi yunƙurin yi wa wasu matan da suka haihu fyaɗe, amma mazan ƙauyen suka kai musu ɗauki.
Wannan ya haifar da rikici inda ’yan bindigar suka buɗe wuta, suka kashe mutum ɗaya tare da raunata wasu.
A ƙauyen Agbami kuma, sun yi wa mutane da yawa dukan kawo wuƙa amma babu wanda ya mutu.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Udeme Edet, ya tabbatar da cewa an tura jami’an tsaro zuwa yankunan da abin ya faru a Makurdi.
Ya ce za su ci gaba da bai wa ’yan jarida bayanai, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani ƙarin bayani.